Thursday, October 17, 2019

AUREN TAGWAYE

[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
           ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
              ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                  ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                     ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                         ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป

*Amincin Allah ya tabbata ga wad'anda zasu karanta wannan labari nawa dama Wad'anda basu samu damar karantawaba ina maku fatan Alkhairi akodayaushe*

~Note~
*Wannan labari 'kir'kirarane banyi dan wani ko wataba, ko satar fasahar wani saboda haka duk Wanda/wacce taga yazo dai-dai danata abune yazo d'aya sai ha'kuri*

*GARGA'DI*
```Ban yarda wani ko wata yayi amfani da wannan labari nawaba ta wata siga saida izinina idan kuma akayi bada iziniba, ban yafeba saboda haka akiyaye```


"Hassana waike bazakiyi sauri mutafiba ke kullum idan mutum yahad'a abu dake sai ranshi ya 6aci, yanzu dan Allah so kike daddy yadawo yahanamu fita, kuma sanin kankine muddin idan banje *Dinner* d'innan ba zuby bazataji dad'iba kinsanfa bikinnan na best friend d'inta ne, kuma ta gayyacemu ba dad'i mu'ki attending.

Cikin sanyin murya wacce aka kira Hassana take magana "Haba Hussaina nifa wlh banison wannan abun dakikeyi, ke shikenan koda yaushe da an gayyaceki ferty kin dinga 'kyarma kenan kamar wacce aka gayyata zuwa aikin hajji.

Magan-ganun Hassana suka 'kara harzu'ka Hussaina cikin bala'i da d'aga murya take cewa "dallah malama kada ki gayamin magana, ke dama duk wata harka ta wayewa baki santaba, idan bazakiba basai kin gayamin maganaba kawai ki zauna a gida, haka zaki 'kare, kullum kitchen.

Zama Hassana tayi bakin gado tare da cire mayafin data sanya, "nikam bazaniba kitafi kawai sai kindawo, ni dama wlh hankalina be kwanta da tafiya wannan *dinner* d'inba kiduba agogo yanzufa 'karfe bakwai da rabi na dare.

Jin Hassana tace bazataba yasa Hussaina zuwa kusa da ita ta du'ko dai-dai fuskarta har numfashinsu na gauraya dana juna, sannan tafara magana cikin sanyin murya.

"Haba my sweet sister, plz ayimin ha'kuri kinsan bazan iya tafiya batare dakeba......

Ringing d'in wayarta ya katseta da maganar datake, da sauri tasa hannu ta d'auko sunan Zuby tagani yana yawo kan screen d'in wayar da sauri ta danna OK tare da karawa a kunne.

"Hellow Zuby ya?
A d'aya 6angaren zuby ta amsa 
"Haba 'kawata me kike har yanzu baki fitoba, halan wannan sister taki ce take maki kofsi.
Hussaina kallon Hassana tayi sannan tace "a'a yanzu zamu taho, tare da itama zamuzo.
"Dan Allah kuyi Sauri.
"Owk kawai Hussaina tafad'a tare da tsinke kiran.

A Falo suka tarad da momynsu tana kallon tashar sunnah TV, cikin ladabi sukaje gabanta Hassana tace "Momy zamu tafi.
Momy ta kalle yaran nata daga sama har 'kasa babu wata shiga ta aibu tattare dasu, atamface suka sanya d'inkin Riga da zani pieces, sai wadataccen gyalen da suka yafa.

"To amma kada Ku wuce 'karfe tara kunsan dai tara da rabi dadynku yake dawowa gida, Momy tafad'a tana 'karemasu kallo, 
Hussaina ce tayi saurin cewa "kada kidamu Momy Tara a gida zatayi mamu.
Hassana tace "insha Allah Momy munyi maki wannan al'kawarin.
"To shikenan kuje Allah maku Albarka 
Tare suka amsa da Ameen sannan suka fice daga gidan.




Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿปshoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------2

Suna fita get sukayi 'yar tafiya kad'an sukasamu napep suka fad'a masa inda ze kaisu.


Lokacin dasuka 'karaso had'addiyar Hotel d'in da'ake gudanar da *dinner* d'in kai tsaye suka nufi hall d'inda suka tabbatar da nanne ake farty saboda mutanen dasuka hango ciki.

Suna shiga lokacin Zuby na zaune suna labari itada wani boy friend d'inta wanda tadad'e da afkawa kogin 'kaunarsa tasha nuna masa haka amma ya'ki yagane dan kwata- kwata Zuby bata cikin tsarin kalar yan matan dayakeso kawai dai yabarta a matsayin Friend.

Cike da farinciki Zuby ta tarbo 'kawarta Hussaina, ko kallan Hassana batayiba, Hassana ma nunawa tayi batasan da zaman wata halitta wai ita zuby ba, dan ita dama tun can jininta be had'u dana zuby ba.

Guri suka samu suka zazzauna kan kujerun dake Jere a hall d'in.
Zuby ta kalli boy friend d'inta sannan takira sunansa "Hafiz, ga 'kawayena danake gayama 'yan biyu ne, wannan itace Hussaina wannan kuma itace Hassana tafad'a tana nuna Hassana yayinda itakuma ta kauda kanta gefe dan ko kad'an ita batason a had'ata da wani namiji barantana kuma har suyi wata magana, shiyasa kodayaushe Hussaina da Zubby suke kiranta bata wayeba.

Haka suka zauna zuby sai wani shishshigema Hafiz takeyi tanata mashi surutu, shikuma kwata- kwata hankalinsa be kanta, tunda su Hassana suka shigo idanunsa suke kan Hussaina, yariga yagama fad'awa kogin 'kaunarta, wanda zuby bata lura da hakanba, amma ita Hussainar ta dad'e da d'agowa dashi kodan yanda dasun had'a ido yake sakar mata wani tsadadden murmushi, dama gashi kyakkyawa ajin farko, take itama Hussaina taji takamu da sonshi.

Wani irin kid'ane ya tashi lokacin da Mr DJ ya kunna Speaker's d'insa, wayyo jikin zuby har 6ari yake, dama haka take mayyar rawace duk sun dad'e da sanin haka saboda haka basuyi mamakin hangonta tsakiyar fage ita kad'ai tana caskad'ewaba, ba kunya take rawar sai wani kaso shoki takeyi..... _Lol_

 Lokacin Hafiz yasamu damar yima Hussina magana, "Ya kike 'yan mata, wayyo wani iri Hussina taji a jikinta lokacin da ta tsinkayi muryar Hafiz a kunnenta, a zuciyarta tace "Wow fantastic, nice voice, Ashe dai yanda yahad'u hakama murayarsa ta had'u gaskiya gayen yagama had'ewa.

Lokacin Hafiz yasake magana karo na biyu batare da Hussaina tabashi amsar ta farkoba, "idan bazaki damuba kisakamin numberki ko bayan kin koma gida sai muyi magana,  
Ba musu ta amsa tasakamai numberta, sannan ta mikamar wayar dayake Hafiz gogaggen d'an duniyane gurin amsar wayar saida yahad'o da hannunta, suduka wani irin shock sukaji lokacin da tattausan hannuwansu suka had'u dana juna, kasa sakin hannunta Hafiz yayi sunkai kimanin minti biyu a haka sai itace tayi 'karfin halin zare hannunta daga nashi, kashe mata ido yayi tare da sakar mata wani 'kawataccen murmushi.

Duk abinda sukeyi Hassna batasaniba duk da guri d'aya suke zaune, hankalinta nakan wayartane tana chat a wani group na Zee Mmn khady me suna *Ciwon Ya mace* tanajin dad'in group d'in sosai yanda ake bada shawara me kyau da kuma yanayin abubuwan amfani da ake turowa, ba kamar kuma Had'in kai da 'yan group d'in suke dashi, duk da yanda takejin dad'in chat da *Mmn Ummi da Ameeno, Mmn Ramadan da rukky abdull* hakan behanta duba lokaciba dan kada suyi dare basu koma gidaba, dan yanzuma data duba 'karfe takwas da rabi, tasama ranta takwas da minti arba'in zasu koma gida.

Muryar Hussaina ta tsinkaya "Hassna dan Allah aromin wayarki zanyi kira, bansan credit d'ina yakareba, ba musu Hassana ta mi'kamata "amma gaskiya dakin gama wayar zamu tafi saboda tara takusa kuma kinsan Al'kawarin da muka d'aukoma momy, 
"To kawai Hussaina tace, tawuce tanufi gunrinda akayi parking d'in motoci kamar tana wayar gaske.
Dai-dai motar da Hafiz yafad'amata nan ta tsaya, jingina tayi da motar idanunta akan wayarta.

Tashi Hafiz yayi yabi bayanta, Hassana na kallo amma bata kawo kome a rantaba, iatadai fatanta kawai idan Hussaina tagama wayar datadawo sutafi gida.




Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------3


Bud'e motar Hafiz yayi gidan baya suka shiga, kasancewar motar tanada ba'kin glass bazeba wanda ke waje damar ganin nacikiba dukda dama gurin akwai duhun dare, 

Ac Hafiz ya kunna musu, take motar tad'au sanyi tare da wani daddad'an 'kamshi 
Zaune suke gaf da juna har jikinsu na had'uwa dana junansu, Hafiz ne yafara magana cikin kwarewa da gogewa na yan duniya "Babyna ammafa kin had'u kinganki kuwa kamar matan hurul'ayni, wani 'kawataccen murmushi Hussaina tayi tare dasa hannunta tarufe fuskarta, duba Hafiz yakai kan shantala-shantalan yatsun hannunta wanda yake d'auke da awarwaraye da wani had'adden zobe na azurfa, hannu yasa Yakama hannun nata yamatse a hannunsa, sannan yafara wasa da zoben "kai amma ring d'innan yayimin kyau babyna, amma set ne tare da sarkarki koh?
Yafad'a tare dakai hannunsa kan wuyanta yana wasa da sarkarta, lokacin yagama kashema Hussaina jiki yanda yake shafar wuyanta, ko magana bata iyawa sai maida numfashi datake d'aya d'aya, hakan yabashi damar yin 'kasa da hannunsa zuwa cikin rigarta yafara wasa da breast d'inta, wani irin yarrrr taji ajikinta, saboda ba'kon Al'amarin daya risketa yau, domin Hafiz shine mutum na farko daya fara yimata irin wannan wasan, suna soyayya da Jabeer amma koda wasa beta6a kai hannunsa kan jikintaba, "hakan yana nufin jabeer be iya soyayyabane ko miye....

Tana cikin wannan tunanin taji Hafiz ya rungomota yahad'ata da jikishi, yana rad'amata kalmar "I love you a kunnenta, cikin kasalalliyar murya tace "mee too my Dear, 
"Wow nice my Baby, Hafiz yafad'a tare da had'e bakinsa da nata yacigaba da kissing d'inta.

Dare yafara Hankalin Hassana ya masifar tashi dan tanemi Hussaina ko'ina a cikin hall d'in da wajen hall d'in amma bata gantaba, duk tabi tarud'e, gashi Zuby tunda tashiga fagen rawa batako wai-waiyesuba barantana ta tambayeta kotasan inda Hussainar take gashi tatafimata da waya barantana takirata.
Komawa tayi kan kujera ta zauna tayi tagumi hannu bibbiyu, 

Can Hankalin Zuby yayo kan inda tabarsu Hussaina amma batagansuba sai Hassana wacce tahad'a hannuwa biyu ta tallabe kumatunta kwalla suncika idanunta, da sauri zuby takaraso inda take "Ke ina 'yar'uwarki?  Hassana batajitaba dan tayi nisa cikin tunanin irin hukuncin da daddy ze yanke masu idan yadawo ya tarar da basunan, batakaran suba ranar momynsuma bazata fitaba dan dady mutumne me zafi tsaye yake kan tarbiyar iyalanshi.

Ta6ota zuby tayi "tambayarki nake ina Hussaina?
Sai lokacin tadawo daga tunanin datake "nima wlh ita nake nema dan Allah ki kiramin ita da wayarki danni tatafi da tawa wayar.
"To ina Hafiz? Zuby ta'kara jeho mata wannan tamabayar
"Kinga ni dukansu bansan inda sukeba, nidai dan Allah ki taimaka ki kiramin Hussaina mutafi gida.

Take zuciyar Zuby tabata akwai wata kulalliya tsakanin Hafiz da Hussaina, idan kau hakane lallai Hussaina tad'auko ruwan dafa kanta.

Wayarta ta fiddo daga cikin poss tafara lalubar number Hussaina, kusan kira takwas zuby tayima Hussaina no answer, hakan ba 'karamin 'kular da ita yayiba, batako kalli Hassanaba tabar gurin tana cika tana batsewa.

Ganin dare na'karyi yasa Hassana tambayar wata budurwa kusa da ita "dan Allah 'karfe nawa?
Duba wayar tayi "karfe tara da Monti takwas tabata amsa a ta'kaice.
 

Cike da rud'ewa Hassana tatashi tafita harabar hotel d'in Allah ya taimaketa lokacin wani me napep ya sauke wasu, tagayamshi inda ze kaita, saida suka d'au hanya tafara tunanin inda 'yar'uwar tata tashiga "Toni yanzu mezanfad'ama Momy idan aka tambayeni Hussaina, wasu hawaye suka gangaro kan kumatunta.
"Allah sa dai tana lafiya duk inda take.
Tana cikin wannan tunanin har suka iso 'kofar gidansu batamasan sunzoba saida me napep yace "hajiya mun isofa sannan ta sallameshi tafita daga napep d'in.

Jiki a sanyaye tanufi gidansu, ahankali ta kwankwasa megadi yabud'emata bayan yatambayeta tagayamashi itace.

Ahankali tashiga gidan da sallama Momy tagani zaune tayi tagumi koba tambaya tasan jiran dawowarsu takeyi, ganin Hassana yasa Momy sauke wata ajiyar zuciya, "Alhmdlh ina 'yar'uwar taki take?

Hawaye yacigaba da zuba daga idon Hassana batare databa Momy amsar tambayar datayimataba, cikin tashin hankali Momy ta'karaso inda Hassana take takama kafad'unta "ina take nace? Ko wani abu ya sameta? Kifad'amin......

Ganin hankalin Momy yatashi yasa Hassana goge hawayenta "bawani abu yasametaba kawai na nemeta bangantaba, kuma gashi dare yayi...

"Subhannallah Momy tafad'a Allah sa dai lafiya, kin kira wayarta? "Nima wayata tana hannunta.

Hankali tashe Momy tasa wayarta takira Hussaina itama no answer aka gayamata kamar yanda duk wanda yakira ake gayamai, saida tayi kira kusan na goma sannan Hussaina ta d'auka cikin kasalalliyar murya tafara magana dan lokacin tana jikin Hafiz yagama rabata da rigarta yana 'ko'karin ciremata breziya, 

Cikin fad'a Momy tace "dan Ubanki kiyi maza ki dawo gidan tun kafin dadynku yadawo, batajira me Hussaina zatafad'aba  Momy takashe wayar

Lokacin sukajiyo horn d'in motar Alamar dawowar me gidan, cikin tsananin tashin hankali Hassana tafara magana "Momy dadyne yadawo nashiga ukku tafad'a tana yarfe hannu.

Da sauri Momy tace "maza ki shige d'akinku kada yazo yaga batanan, Dan batakaran itadayi laifinba mu kanmu sai rayukanmu sun 6aci.

Da sauri Hassana tashige d'aki, zama tayi bakin gado tayi tagumi hannu bibbiyu tana tunanin 'yar'uwarta.





Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------5


Jitayi an sha'kota ta baya a firgice ta juyo, ido biyu sukayi da daddy beyi wata-wataba yafara zabga mata cable wayar dake hannunsa nan tafasa 'kara tana ihu, amma daddy be sauraramataba, tsulamata wayar yakeyi iya 'karfinshi, mommy da Hassana suna daga falo sukajiyo ihunta, wani sabon kuka ya kwacema Hassana cewa take "Momy dan Allah ki taimaki Hussaina kiba daddy ha'kuri kada yajimata ciwo, kallonta Momy tayi cikin nuna rashin halin damuwa tace "koma miye ita tajama kanta 'kara yadaketa gobe bazata 'karaba.

 Da gudu tashigo falon kamar wacce aka jeho, bayan Momy tanufa tana kuka ta 'kan'kameta "wayyo Momy dan Allah ki taimakeni wlh bazan 'karaba, 
6an6areta Momy tayi daga jikinta tare da barin gurin tana cewa "lokacin dakikayi rashin jin naki kinyi shawara dani, dan haka kada ki nemi taimakona can ki 'karata jiki magayi, shigewarta tayi d'aki ta maida 'kofarta tarufe,  wani irin kuka Hassana tafashe dashi ganin momy batada niyyar baiwa dady ha'kuri shikuma beda niyyar hakura, rugowa tayi tari'ke hannun daddy tanamashi magiya "dan Allah daddy kayimata ha'kuri bazata 'karaba, a harzu'ke daddy ya hankad'ar da Hassana gefe guda yacigaba da suburbud'ar Hussaina, suduka suke kuka suna bashi ha'kuri amma beko sauraresuba saida ya tabbatar Hussaina ta daku sannan ya rabu da ita yanufi d'akinshi yana huci yana cewa "gobema ki kara tafiya ki wuce magrib baki dawo gidaba wannan kad'an nayima shashasha kawai.

Kama hannunta Hassana tayi suka nufi d'akinsu, da kyar Husaina take tafiya saboda ba 'karamin duka tasha hannun daddynsu ba, 

Zaunar da ita Hassana tayi bakin gado tana sharar kwallah, tace "kinga abinda nake gujemaki koh, ba irin neman dabanyimaki gurin *dinner* d'innan ba amma ban gankiba, wai ina kikajene?

Cikin dasashshiyar murya Hussaina tace "uhm yanzu banida lokacin dazanbaki wannan amsar, 
Toilet Hassana tanufa batare data 'karama Hussaina wata maganaba ruwan d'umi tahad'amata tarakata har toilet sannan tajawo mata 'kofar, haka tayi wanka ta gargasa jikinta bayan tafito Hassana tasa Robb ta shafemata jikinta sannan sukabi lafiyar gado, kowace tayi shiru kamar me bacci a zahiri amma kowace da tunanin datake cikin zuciyarta, Hussaina tunanin Hafiz ne fall cukushe a zuciyarta, "lallai Hafiz ya iya soyayya, yanzu nagane jabeer ba kome ya iyaba a fanni soyayya sai dai kullum idan yazo yakamayimani nasiha da sauransu, nikam nafison namiji d'an life Wanda yasan takan love, gaskiya akwai sakal kan maganaraurean da jabeer dan ni yanzu babu namijin danake muradi a rayuwa kamar Hafiz, dan Abinda ya faru tsakaninmu yau yasa naji bana bukatar kowane namiji sai shi.

Hassana kuwa tunani take shin ina 'yar'uwarta tashiga har takai wannan daren bata dawo gidaba, Allah sa dai Hussaina bata biyema samarin shahoba, mayaudara "Hmm tafad'a shiyasa niko Alama bana harkar samari.
Da haka ta gyara kwanciyarta bacci yayi awon gaba da ita.

6angaren dady kuwa bacci gagaran idanunsa yayi tashi yayi ya zauna gefen gado ya zabga uban tagumi, zuwa can kuma yami'ke tsaye yafara safa da marwa cikin d'aki, "lallai dole inyi saurin yima tufkar hanci, saina tashi tsaye kan tarbiyar yaranan, saboda zamaninnan yanzu saika haifi d'a baka haifi halinsaba. Kusan raba dare daddy yayi yana tunani.

**           **           **        **

Washe gari zaune suke kan dining suna breakfast bakajin motsin kome sai 'karar plate da cokulla, kowane ka kallah cikinsu rai a dagule dakuma tunanin abinda yafaru jiya.

Bayan sun kammala daddy yayi gyaran murya "kunajina? Suduka suka jiyo suka kalleshi, "tunda abin naku yazama lalata inaso insanar daku na soke maganar makarntar dazakuje *AMUSLIM COMMUNITY SCIENCE &TECHNOLOGY FUTUA* daga yau kucireta a ranku kuduka aure zanyimaku, ke Hassana inaso kifito da miji nanda wata d'aya, ke Kuma Hussaina ya watsamata wani matsiyacin kallo "kigayama jabeer inason ganinshi, wani irin Fad'uwar gaba Hussaina taji dajin dady yace yana neman jabeer, sadda kai tayi 'kasa "daddy nifa mundad'e da 6atawa da jabeer.

Shiru daddy yayi yana kallonta, toki fiddo miji nanda wata d'aya, idan kika wuce iya adadin kwanakin dana ebar miki zand'au duk matakin danaga ya dace.

Mi'kewa yayi tare da d'aukar jakarsa ta zuwa office sannan ya kalli Momy "maganar fita kuma daga yau nakasheta idan sunbar gidannan a tabbatar islamiyya zasu, yana gama fad'a yasa kai yafice.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป Shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------4


Hassana na daga d'akinsu taji shigowar daddy wani mummunan fad'uwar gaba taji, tanajin lokacin da Momy kemasa sannu da zuwa, yana zama ba abinda yafara tambaya sai "Ina yarannan suke? Cikin inda-inda Momy tabashi amsa "uhm am suna d'akinsu ko Alh....

Kwalamasu kira yashigayi "Hassana....Hussaina....
Hassana naji tayi saurin Amsawa "na'am...
"Kuzo nan ina nemanku "to ta amsa jiki na kyarma tasako d'an karamin hijab d'inta ta fito, durkusawa tayi gaban daddy "gani daddy tafad'a tare da sunkuyar da kanta 'kasa gabanta sai dukan tara-tara yake.

"Ina 'yar'uwar taki? Daddy ya tambaya, "im ahm....uhmmm tafara inda-inda tarasa wace amsa zata bayar domin kare 'yar'uwarta shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta.

Tsawa daddy ya kwatsa mata "ke.... Ba magana nike dakeba ina 'yar'uwarki nace? Jiki na 'kyarma tafara magana tana d'an ja da baya dan taga yanda daddyn nasu ya zuciya a lokacin ze iya mazgeta, "daddy munje walimar bikin wata 'kawarmune shine dazan taho nayita nemanta bangantaba shine nikuma nataho, 
"Owk good hakan yayi kyau, shine ita ta zauna dan bata tsoron fushina, aiko ranta inyayi dubu a gidannan yau sai ya 6aci, kallon Momy yayi "kekuma kinsan bata dawoba amma ko ajikinki saboda baki damu da tarbiyar yarankiba ko "haba Alhj ya zakace bandamu da tarbiyarsuba, wlh tun d'azu nake faman kiran wayarta sai tacemun gatanan to ya kakeso inyi? Ko zuwa zanyi intaho da ita, 
"A'a ba tahowa zakiyi da itaba, idan bakije kika taho da itaba nizan taho da ita dakaina, yafad'a yana nuni da 'kirjinshi da hannu.

Bejira abinda zatafad'aba ya zari cable d'in jikin tv yafita zuwa harabar gidan, 
Me gadi na hangoshi tafe yataso da sauri "Sannu da fitowa Alhj, "yauwa mal bala, abinda kawai ya furta kenan sannan yafita daga wajen get d'in gidan ya tsaya ya maida hannuwanshi duka baya, yafara safa da marwa yana jiran yaga ta ina Hussaina zata 6ullo, tsawon kimanin minti goma sha biyar yana zarya gurin Amma bako Alamarta, mal bala me gadine ya le'ko cikin girmamawa yafara magana "Alhj lafiya kuwa naganka haka kamar hankalinka a tashe?
"Mal bala yarinyarnan ni zata rainama hankali ni zata maida mutumin banza cikin garinnan, da darajata da 'kimata ace wai har kamar 'yanzu 'karfe goma da minti ashirin da takwas yarana suna gantali a gari.
 Mal bala yace "amma Alh ai naga kamar sundawo ko? "Gudace tadawo yanzu jiran dawowar d'ayar nake.
"To Alhj Allah maidota lafiya, Allah sa duk inda take tana lafiya.
Komawa mal bala yayi daga ciki ya zauna kan d'an bencinshi, yanda hankalin Alhj yatashi shima duk sai yajishi cikin damuwa, saboda Alhj mutum ne harda rabin mutum.

Da misalin 'karfe sha d'aya saura minti goma, lokacin Alhj yagaji da zarya tsakanin wajen get d'in gidan zuwa cikin gida, yana zaune kan bencin mal bala, tsayuwar mota yaji dai-dai get d'in gidansa da sauri Alhj ya mi'ke le'kawa yayi lokacin Har Hussaina tafito daga motar me motar yayi gaba abinsa, 

Momy kuwa da Hassana suna cikin gida hankalinsu a tashe, Hassana banda kuka ba abinda takeyi.

Hussaina kuwa bayan Hafiz ya ajiyeta ya wuce sai lokacin wani mugun tsoro ya dirar mata cikin zuciya, jikinta yafara 'kyarma, hankalinta be 'kara tashiba saida taduba agogo taga 'karfe sha d'aya na dare, ahankali tafara buga get d'in gidan, da sauri mal bala yazo ya bud'e mata tana Shiga,tafara tafiya da sauri tana wai-waye saida tazo gab dashiga falon gidan ta tsaya tacire takalminta dan kada ajiyo 'karar tafiyarta, ri'ke takalmin tayi a hannu sannan tatura 'kyauren falon ahankali.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------6



      *Bayan sati d'aya*
Hassana da Hussaina sun daina fita konan da can kullum sai dai idan zasu islamiyya, maganar fitar da miji kuwa kullum sai daddynsu ya tinasar dasu, 

Yauma kamar kullum zaune suke kan had'addun kujerun dake zagaye da babban falon gidan, Hassana ta kalli Hussaina, "nikam sister inaso muyi wata magana dake, 
"Ina jinki Hussaina tafad'a, 
"Wai meyasa kikacema Abba kun 6ata da jebeer Alhalin ba abinda yashiga tsakaninku, 
Murmushi Hussaina tayi sannan ta d'au 'kafa d'aya ta d'ora kan d'aya tana girgizawa "ba wani dalili kawai tsuntsun 'kaunarsane ya canja she'ka.

Tana fad'in haka ta maida hankalinta kan wayarta wacce suke chat itada Hafiz suna tattauna yanda za'ayi su had'u dan tun ranar da daddy yahanasu fita tasanar dashi, shikuma kullum sai yakirata yakai sau goma yanamata magiya akan dan Allah tayi dabarar dazasu had'u koda na minti biyar ne.

Sauke ajiyar Zuciya Hussaina tayi, tace "amma Hussaina idan kikayima jabeer haka kinci amana, kinriga kinsan irin so da 'kaunar dayake nunamaki, zeyi wuya kisamu namijin daze soki kamar jabeer.

"Ba wani wuya, Hussaina tafad'a saboda nadad'e dasamun wanda ya mayemin gurbinsa, cike da mamaki Hussaina ta kalleta wannan wanene wanda yayi 'karfin halin raba Zukatan dasuka dad'e suna maradin zama abu guda, 

"Murmushi Hussaina tayi tare da mi'kewa tsaye tayi taku biyu zuwa ukku sannan tajuyo ta kalli Hassana wacce kebinta da ido tana jiran jin amsarta "Ba wani bane kinsanshi, Hafiz Wanda muka had'u dashi gurin *dinner* itama Hassana mi'kewa tayi ta isa inda Hussaina take cike da mamaki "indai Wannan Hafiz d'in kike nufi wlh inabaki shawara da kada kiyi sakin na  hannu kamun na guje danni wannan Hafiz d'in da kike gani kwata-kwata be kwantamin araiba da ganinshi yafi kama da yan abi yarima asha kid'a,

Hannunta takai kan kafad'ar Hussaina ta dafata "sister iname baki shawara kada kibari jabeer ya su6uce maki dan samun namiji kamarsa a wannan zamanin sai antona......

"Ke dakata, hussaina tafad'a cikin d'aga murya, kada ki kawomin 'kabli da ba'adi nace banison jabeer idan ke kinasonshi ki aureshi mana wani yahanaki, "Hmm aini tun farko bani yace yansoba, amma in bancin haka banga abin 'ki gareshiba.

"Mtsswww, Hussaina taja wani dogon tsaki sannan tanufi bedroom tabar Hassana nan tsaye cike da mamakin hali irin na 'yar'uwarta.

Hussaina kuwa tana shiga d'aki kiran Hafiz yashigo wayarta, cike da farinciki ta d'auka bayan ta sumbaci wayar dan a kullum 'karajin son Hafiz takeyi cikin zuciyarta.

"hellow babyna, 
"uhm my dear ya kake tafad'a cikin shagwa6a.
"Eh to gaskiya ba lafiya...
"subhannallah meyasameka tafad'a tare da gyara zamanta.
"kin'ki muhad'u dan baki d'auki son danikemaki a bakin komeba.
Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke "Haba my dear dan saboda wannan zakace bakada lafiya, indai wannan ne ka kwantar da hankalinka yau idan nafito islamiyya zamu had'u.
"Wow babyna amma naji dad'i, 'karfe nawa kuke fitowa?
'Karfe hud'une mukoma shidda, kaga wannan lokacin ya ishemu mud'an gaisa.
"Eh to hakane amma kinsanfa nayi missing d'inki sosai.
"Hmm sai munhad'un kawai tafad'a 
"Owk bye "muaaah yasakar mata wani kiss ta wayar sannan ya tsinke kiran, wani dad'i taji ya ziyarci zuciyarta rungume wayar tayi cike da Farin ciki, harta 'kosa Hud'u na yamma tayi sufita zuwa islamiyya.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป๐Ÿ˜‚
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------7


Da misalin 'karfe hud'u saura minti goma Hussaina tagama shirinta tsaf na islamiyyah cikin uniform kalar ruwan 'kasa, 

"Kallon yar'uwarta tayi wacce ke 'ko'karin d'aura farin d'an kwali, tace Hassana kiyi sauri kinga bana bu'katar zuwa a makare, kallo kawai Hassana tabita dashi "Tofah yau kuma kece me cewa bakison makara ince kullum saina gama shiryawa sannan inyi zaman jiranki, 
"Naji dan Allah yanzu dai kitaho mutafi kina 'kara tsyar damu, ......
Dai-dai lokacin kuma wayarta tayi ringing dubawa tayi jiki na kyarma takai dubanta ga Hassana wacce tagama shirinta tsaf tana jiran sutafi.

Sunan Hafiz tagani yana yawo kan wayar, dama kuma kobata dubaba tasan shine dan tsakanin 'karfe ukku da Rabi zuwa yanzu 'karfe hud'u yayimata kira yakai tara,
"Hellow yanzu zamu fito daga gidan, tafad'a tana kallon Hassana ta wutsiyar ido,
"To babyna dan Allah kiyi sauri wlh na matsu na ganki dan bakisan yanda nakejibane shiyasa kikai har yanzu baki fitoba.
"Sorry dear ina hanyafa nace ka saurareni mana.
"To shikenan ina gurinda nagayamaki, 
To sainazo tafad'a tare da kashe wayar.

Tana juyowa suka had'a ido da Hassana saida gabanta yayi 'yar 'karamar fad'uwa saboda kallon tuhumar dataga tana mata. 

 Nunawa tayi kamar batasan kome kenanba tace "muje ko kada mu makara naga yau baki bu'katar muyi latti, 
"Owk muje to.

Haka suka jero gwanin ban sha'awa kome nasu iri d'aya ga tsananin kamanni dasuke farinsu d'aya tsawonsu d'aya haka zubin jikinsu d'aya, suna matu'kar kamanni wanda hakan kesawa mutane da dama basa gane Hassana basa gane Hussaina, hatta da iyayensu basu cika ganesuba saita gurin halinsu daya bam-bamta.

 A falo suka tarar da Momy, cikin ladabi suka isa gabanta "Momy mutafi islamiyyah 
"To Allah bada sa'a Yakuma tsareku, Allah yayimaku Albarka, Adawo lafiya.

Amsawa sukayi da Ameen sannan suka fice, suna fita sukasamu me napep suka gayamashi sunan islamiyyar daze kaisu, 

Sun fara tafiya Hussaina ta Kalli Hassana tace "sister dan Allah kiyimin taimako d'aya sonike inje gidansu zuby kuma kinsan gida baza'abarni infitaba inaso me napep ya saukeni acan sai awuce dake islamiyya idan antaso kimin waya sai muhad'u mutafi gida.

Da Hassana kamar bazata Aminceba saikuma tace "to shikenan Amma dan Allah kada ki wuce lokacin tashinmu islamiyya, kinsan dai daddy ba sauki.
"InshaAllah kinamin waya zanzo, "to shikenan.

Hassana aka fara saukewa islamiyya sannan aka wuce da Hussaina unguwar Barhim dake wajen Gari, dai-dai inda Hafiz yagayamata yananan nan kuwa tasameshi.

Tana fitowa daga napep ta hangoshi tsaye jikin motarshi ya hard'e duka hannayenshi a 'kirji, sanye yake cikin bakin wando, da yellow riga, sai ba'ka'ken takalmi, sannan ya d'ora wani ba'kin glass Wanda ya'kara fitowa da ainafin kyawunsa.

Yana hangota yafara jefarta da 'kawataccen murmushinsa, itama maida mashi martani tayi harta isa gurinshi suna musayar murmushi.

"Welcome babyna yafad'a tare da rungumata a jikinshi, saurin tureshi tayi tana  waige kada ace mutane suna kallonsu. *{Hmm Hussaina kenan idan mutane basu ganinku ai Allah yana ganinku}*

"kada kidamu babyna ba mutane sosai a unguwar, kodama wani yaganmu ba wanda ze shiga harkarmu, amma tunda naga kamar kina tsoro shigo daga ciki, "dadai yafi, tafad'a
Sannan yabud'emata motar tashiga shima yashiga.







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------9


Bayan shigowar jabeer suka gaisa da Momy sannan tashige d'akinta tabasu guri, Hassana ce tacika gabanshi da kayan ciye-ciye dana sha, sannan tad'an zauna domin su gaisa, lokacin Hussqina tana zaune tabi ta had'e girar sama data 'kasa sai danne-danne take a wayarta, 

Shiru ya gifta nayan wasu mintoci, Hassanace ta katse shirun ta hanyar cewa "Yaya jabeer ina wuni, 
"lafiya lao ya Amsa yana 'karemata kallo, a zuciyarshi yana cewa wannnan itace hassanar kokuwa Hussainar ce, saida yaji tami'ke tsaye tana cewa "to nikam nashiga daga ciki sannan yagane ashe ga mutunniyar tashi nan gabanshi wacce tunda yashigo ko kallo be ishetaba, taunar cingam kawai take sannan hankalinta duka yana kan wayarta tana ibadar wato chat da Hafiz.

 Shiru sukayi suduka anrasa wanda zefara magana dan Hussainama yau ko arzi'kin gaisuwa Jabeer be samuba, illah wani irin haushinsama datakeji dan tadad'e dagayamshi maganar soyayyarsu ya janye ya nemi wata Amma dayake shine d'an anace sarkin naci ya'ki ha'kura.

Jabeer ne ya katse shirun ta hanyar cewa "jiya naga fitarku lokacin zaku islamiyya naso inyimaku magana amma sainaga rashin dacewar hakan kasancewar gurin dazaku yanada muhimmaci bekamata ace na tsaidakuba.
"Hmm aikode, kawai tafad'a tare da yamutsa fuska ta juyar da kanta gefe tana taunar cingam 'kas-'kas
Har cikin ranshi yaji haushin yanda tayi Mashi magana amma sai ya danne kasancewar anason namiji yazama me shariya akan wasu 'kananan abubuwa, magana ya'kara karo na biyu.

"Gaskiya inajin dad'in yanda kuke zuwa islamiyyah fatana akodayaushe kafin Aurenmu ace kunyi safka kunyi hadda koda hizif talatin ga sauran litattafan addini, kinga ko'ina zanyi Alfahari da matata tanada ilimin addini, sannan kuma uwa uba yaranmu zasu koya a gun mamarsu kafin suma asakasu tasu islamiyyar.....

Dakatar dashi tayi ta hanyar d'aga mashi hannu tana magana cikin masifa "dakata malam, wai akan wa kake magana? "Ni, tanuna kanta da hannunta, to indai nice kama daina wannan tunanin kacire soyayyata daga cikin zuciyarka, danni yanzu batakai nakeyi 'karama kanemi me sonka tunda wuri kafin lokaci ya'kurema.

Haba Hussaina donmi kike nema ki gujeni? Menayimaki? Kadafa ki manta mundad'e muna soyayya kullum burinmu be wuce muzama mata da mijiba, amma yanzu Cikin 'kan-'kanin lokaci kina nema ki canja ra'ayi.

"Oh nema manake incanja, tobari kaji in gayama ba nema nakeyiba nama canja gaba d'aya yanzu baka cikin tsarin mazan danike burin aure...
Tuni kuma wani ya maye gurbinka acikin zucyata saboda haka kaje kawai kanemi wata,

Cike da mamaki da takaicin yanda Hussaina ke gayamar magana yabar gidan, dan kosamun damar yin bankwana da Momy beyiba, 

Dai-dai harabar gidan suka had'e da Zuby tana shigowa "tana ganin jabeer ta washe baki "a'a'a Manya kenan anzo gun mutuniyar, dariyar ya'ke kawai ya 'ka'karo Wanda hakan baze hana kagane cikin tsananin damuwar dayakeba, 
"Eh wlh kuma gashi harna fitoba, to shikenan agaida gida.

Tana tsaye yashige motarsa yatayar da ita Malam bala me gadi yabud'emashi get yanatayimar fadanci dan yasaba duk ranar dayazo yakan bashi nacin goro amma yau sai yaga Alamar ranshi kamar a 6ace yake, haka yabar gidan Malam bala yamaida get yarufe sannan yakoma kan bencinsa yazauna yana cewa "ho yar nema yau ta6atama mutumin rai 'yan aninnan danike samuma yau bansamesuba, sannan yajawo redio ya kunna yana saurare.

Zuby kuwa taso taji wani abu daga bakin jabeer amma ganin ranshi a 6ace kuma bebata fuskar hakanba yasa tayi ciki tana zumud'in ji daga bakin 'kawarta.










Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿปshoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------8


Rungumota yayi jikinsa tare da d'ora lips d'insa kan kumatunta yasakar mata kiss, 
"Kinsan wani abu babyna? Yafada cikin had'addiyar murayarshi me kashe mata jiki.
"A'a saika fad'a my dear.
"Gaskiya naji dad'i nayi matu'kar farinciki yanda kika amince kikazo inda nake yanzu na'kara yarda da 'kaunar da kikemun hundred percent, wani irin dad'i taji har cikin ranta sannan tafara magana cikin kasalalliyar murya,
"My dear inaso ka yarda dani kamar yanda na yarda dakai, 
"Na yarda dake babyna yafad'a tare da saka hannunshi d'aya cikin hijab d'inta yafara wasa  da dukiyar fulaninta, hannunsa d'aya kuma nakan cikinta yanamata wani salo wanda ke 'kara rikitata, 

Suduka sun lula duniyar soyayyar shan minti, bakajin komai sai numfashi dasuke maidawa sama-sama, haka sukayita wasanni tsakaninsu tare dajin dad'in kasancewa da juna.


Hassana kuwa tana islamiyyah suna karatu, bayan malamin dake d'aukarsu darasin Qur'an yafita sai me d'aukarsu hadith yashigo, saboda haka tana ganin haka tasan lokacin tashinsu yakusa dan dama hadith shine period d'in 'karshe kuma baya dad'ewa lokacinsa ke 'karewa saboda haka kafin yafara karatu ta d'auko wayarta sunan Hussaina ta lalubo sannan ta dannan kira.

Lokacin Hussaina na jikin Hafiz yariga yagama tayar mata da hankali kwata- kwata bata cikin hayyacinta har wayar takaraci ringing d'inta tagama bata d'agaba, sai a kira na ukku sannan tad'aga 
"Hellow sister antashine, "eh kitaho muhad'e yanda zamu koma gida tare.
"Owk ganinan zuwa.

Bayan ta tsinke kiran ta maida dubanta ga Hafiz "yauwa my dear dama inason magana dakai, 
"Ina jinki babyna.
"Bawata magana bace dama daddynmune yace yabamu wata d'aya mu fitar da miji, nikuma ba wanda nakeso sai kai shine nace yakamata ka gabatar da kanka gareshi.

Shiru yayi kamar me tunanin wani abu, itakuma ta zubamar ido tana jiran amsar daze bata, ganin beda niyyar yin magana yasata ta6oshi "dear lfy naga kayi shiru kobakaji me nake fad'a bane.

"Murmushi yayi "najiki babyna, kada kidamu aini dama irin wannan ranar nake jira, zanzo inshaAllah kada kiji kome aini me 'kaunarkine.
"Wani irin murmushi tasakar mashi cikin farin ciki sannan taduba wayarta 'karfe shidda saura minti goma a gaggauce sukayi bankwana yabata iyayen kud'i ta'ki amsa saboda tana tsoron gida aganta dasu.
Me napep ta tsaida tashiga zuwa gidansu.

Yana ganin tafiyarta ya kece da wata irin dariya tare dakaima sitiyarin motarshi duka "wow Allah kai damo ga harawa kobeciba yayi birgima, kowa yagayamata zan iya auren macen danagama lugui-guitawa a waje, aini sai kamilar mace wacce tasan darajar kanta ba irinkiba wacce zatabi namiji har inda yake.
A haka yatashi motarsa ya 'kara gaba ranshi fari tass.

Hussaina kuwa napep na ajiye Hassan itama ana ajiyeta, saboda haka tare suka shiga gida babu wata matsala.

   *washe Gari*
Da misalin 'karfe hud'u da rabi na yamma Zaune suke falo suna kallon gidan tv startime tashar farin wata suna shirin addini da Alqibla, kasancewar yau Alhamis ba islamiyyah suduka hada Momy duk sun maida hankalinsu kan shirin amma banda Hussaina wacce hankalinta yana kan waya tana chat da Hafiz Wanda yawanci magan-ganun duk na shan mintine sukeyima junansu.

Tsayuwar mota sukaji a harabar gidan, da sauri Hassana ta le'ka ta window kafin tadawo ta zauna ta dubi Hussaina, tace "jabeer nefa yazo, cigaba da chat d'inta Hussaina tayi bata ko kalli Hassanaba barantana tabata amsar maganar datayimata.

Ganin batada niyyar motsawa yasa Momy cewa "ba magana ake makiba kobakijine jabeer ne yazo, 
Turo baki tayi ni wlh momy wannan jabeer d'in yadameni nifa nagayamashi yanzu bani sonshi ko ana dole ne...... 
Bugemata baki momy tayi "banison sakarcin banza idan kince kin daina son jabeer wa kike dashi wanda yafishi, yaro mutumin kirki me hankali ga nutsuwa, saboda hakama mahaifinku yad'aukeshi tamkar d'an cikinsa.

Tashi tayi tana dira 'kafa cikin shagwa6a ni Momy nafad'amaki inada Wanda nakeso kuma ai yace zezo ya gabatar da kanshi gurin daddy.
"Keni rufemin baki sakaran banza.

Momy ta kalla  Hassana "jeki shigo dashi, 
"To tafad'a sannan tanufi 'kofa tana kallon Hussaina
Wacce tadage ita a dole batason jabeer hadda yan guntayen hawayenta.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿปshoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------10



Da sallama Zuby tashiga falon gidan Har yanzu Hussaina na zaune inda take sai cika takeyi tana batsewa, kallonta Zuby tayi "kawata lafiya naganki haka ko wani abune yafaru.

Kedai bari 'kawata wancen mutumin mana yazo ya dagulamin lissafi, 
"Wane mutumi kuma Zuby ta tambaya tare da nuna rashin gane inda abin yadosa.

Haba wane mutumifa banda jabeer, nafa dad'e da gayamashi na daina yayinshi yaha'kura Amma yanacemun,
"haba 'kawata miye aibun jabeer da zaki 'kishi jabeer kau ai namijine na nunama tsara, ga kyau ga wayewa.

"Amma kuma kwata-kwata be iya soyayyayba, Hussaina tafad'a ni kalar soyayyarshi bataminba, kinsan nasha gayamaki nafison namiji d'an life wanda yasan takan love.

"To amma tuni baki gane hakaba kike tare dashi sai yanzu.
"Kwaraiko saboda yanzu nasamu wanda ya iyane shiyasa nagane shi be iya komeba.

'Kara matsowa Zuby tayi tare da d'ora hannunta kan cinyar Hussaina "Amma 'kawata wanene wannan wanda yayi sa'ar saye zuciyarki cikin 'kan'kanin lokaci.

Wani 'kawataccen murmushi Hussaina tayi "Hafiz" wani mummunan fad'uwar gaba Zuby tayi dukda ta dad'e da sanin akwai soyayya tsakanin Hussainar da Hafiz, 

"Wane Hafiz ? Ta tambaya danta 'kara tabbatarma kanta abinda Hafiz d'in yagayamata gaskiyane, Hafiz mana Wanda Muka had'u ranar *dinner*  wani busashshen murmushi Zuby ta 'ka'karo "kai amma dole kike susucewa 'kawata ai Hafiz gwanine kan soyayya ga kud'i ga kyau ga kuma harkar wayewa.

"Shiyasa ai nakamu da sonshi cikin 'kan'kanin lokaci saboda iya soyayyarshi amma kin had'a da wancen bagidajen shi kullum yazo beda magana sai wa'azi da sauka da Hadda kamar shine yasakani islamiyyar, kwashewa sukayi da dariya tare da tafawa, "wlh kuwa 'kawata yo ko dady dayasakamu islamiyyar beyimana bin diddigi irin nashi.

Sai gab da magrib sannan zuby tabar gidan, Zuciyarta tana tunanin Hanyar dazatabi ta 'kuntatama Hussaina tunda harta yarda tayi soyayya da Hafiz mutumin datafiso tafi 'kauna akan kome da kowa,  


         *Bayan kwana hud'u*

Zaune Suke a mota itada Hafiz suna soyayyarsu kamar yanda suka saba.
 yauma sunfito islamiyyah tayima Hassana 'karyar cewa Zata gano mamar Zuby da aka kwantar da ita asibiti, shinefa tataho inda suka saba had'uwa.

Rungume take jikinsa da kyar tasamu ta kwace daga jikinsa sannan tamaida dubanta gareshi,
"Nikam Hafiz narasa gane kanka koda yaushe idan nace kanasona kace kanasona amma har yanzu ka gagara zuwa gidanmu ka gabatar da kanka ga mahaifina kullum ina sanar dakai lokacin da aka ebar mana yakusa 'karewa ko jiya saida daddy ya'kara mana tuni saura kwana goma idan bamu fito da mijiba ze za6a mana da kanshi, nikuma kasan bazan iya rayuwa da wani namijiba idan bakaiba.

"Kada ki damu babyna nima ina sonki kuma bazan iya had'a soyayyarki data kowace maceba, maganar gabatar da kaina ga iyayenki kuma akwai dalilin dayasa kikaga har yanzu banjeba.

"Haba my dear wannan wane daliline haka?

Kinsan dad d'ina yana 'kasar Cairo hajiyatace ke mana kome to jiya nayimata maganarki shine take cewa inkawoki Ku gaisa kafin manya sushiga maganar, tonikuma ina tsoron gayamaki dan naga had'uwarmuma dayaya mukeyi barantana kuma ace zakije gidanmu.

"Haba my dear indan wannan ne kada kadamu zanzo "haba yaushe to?
"Yaushe kakeso inzo
"Zaki iya fitowa gobe, 
"Badamuwa kajirani anan, amma sai antashi islamiyyah zantaho, "to badamuwa.

Da haka sukayi sallama tahau napep tanufi islamiyyarsu suna isa ana taso dalibai saboda haka Hassana suka d'auka sannan suka wuce.  







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป Shoki ๐ŸŠ๐Ÿป 

๐Ÿ˜ƒ *Kada kudamu da shokina reader's sanyine kawai ke aiki* ๐Ÿ˜‚
*08166169254* for comment
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------12


'Daukarta yayi d'af daga kan kujera yanufi bedroom da ita, shimfid'ar da ita yayi kan gado ranshi fari tas wasanni yafara mata yana shafa jikinta ko'ina yakai kimanin minti talatin yana mata haka, lokacin yagama rikicewa yakai 'kololuwa gurin sha'awa, juyar da ita yayi sannan ya zuge zip d'in rigarta kasancewar zip d'in irin me 6allewane yasa besha wahala gurin cire ainafin rigar dake jikintaba, sannan ya kwance mad'aurin zaninta yarage daga ita sai breaziya sai kuma undi 'ko'karin ciremata undi yashigayi, saida yarabata da kome na jikinta bayyanar surar jikinta ya'kara rikirkitashi, yashiga aikamata da sakonni yana wasanni da ita.

Lokacin shima yacire duk wani kaya dake jikinshi shorniker kawai yaragemar, yana 'ko'karin cire shortniker dinne dan yamatsu yacimma burinshi na sanin Hussaina a matsayin mace, lkoacin kuma wayarshi tashiga ringing.
Hannu yasa ya d'auka ganin sunan 'kanwarsa na yawo kan screen d'in wayar yasa yayi saurin d'agawa tare da karawa a kunnensa "Hellow Fatima ya'akayi? Ya tambayeta cikin tsananin jin haushin kiran datayimashi lokacin dayake burin cimma manufarshi.
Cikin muryar kuka Fatima take magana "Yaya kayi sauri kazo gida yanzu jikin hajiyane yatashi ahalin yanzu batasan inda kanta yakeba.

Subhanallah yafad'a tare da saurin mi'kewa ya rarumi kayanshi ya maida bekobi takan Hussainaba wacce taketa sharar bacci tsirara haihuwar uwarata kan gado.



A gidansu Hussaina kuwa Hankalinsu yayi matu'kar tashi ganin 'karfe goma ta gota ba Hussaina ba labarinta, gashi ko ankira wayarta switch up, 

Daddy yagama 'kulewa ranshi yayi matukar 6aci.
"Lallai yarinyar nan tana nema ta maidani mutumin banza cikin garinnan, nizata jama abin magana aiko zata dawo ta tarad dani zatamin bayanin inda taje, 
Sannan ya maida dubanshi ga momy "kece me babban laifi keda kikabarta tafita bayan kinsan dokar dana kafa a gidannan.
"Haba Alh sau nawa zan gayama bansan fitar yarinyar nanba, ko kana tunanin nizan bata izinin fitane, bayan nasan dokar daka kafa a gidannan.

"Zata sameni nikad'ai nasan hukuncin dazan yankemata, kuma kuduka bance wani yabani ha'kuri akan kowane hukunci zan yanke akantaba yafad'a yana nuna Momy da Hassana wacce ba abinda take sai kuka, tana ro'kon Allah ya maido mata da yar'uwarta lafiya duk inda take.

         *12:30am* ⏱

Da misalin 'karfe sha biyu da rabi na dare Hussaina tafarka daga nannauyan baccin datakeyi ahankali ta bud'e idanunta a tunaninta d'akinsu take, kawai sai ganinta tayi wani d'akin daban wanda bazata iya sheda inda take.

"Subhanallahi tafad'a tare da 'karema jikinta kallo ba kome jikinta, saurin jawo zaninta tayi ta rufe jikinta tana waige-waige taga ta inda mutum zefito daga cikin d'akin amma bataga Alamar hakanba, 
Ahankali tunanin abinda yafaru da ita yafara dawomata a kwalwa, sai lokacin ta tuna tazonefa gaida hajiyar Hafiz, to Amma meya kawota nan? Waye yarabata da kayan jikinta? Ganin batada wanda zebata amsar duka jerin wad'annan tambayoyin data jeroma kanta yasata aza hannuwanta duka biyu aka ta kwala wata irin 'kara.
"Shikenan Hafiz ka cuceni kagama da rayuwata ka 6atamin abinda duk wata mace take ta'kama kuma take tin'kaho dashi a duniya, jin damshi-danshi 'kar'kashinta yasa ta'kara tabbatarma kanta da abinda take zargi "shikenan Hafiz yagama dani ya 6atamin budurcina nashiga ukku tafad'a tare da sakin wani wahalallen kuka.

Ahaka ta maida kayanta ta d'auki jakarta koda ta d'auko wayarta kashe taganta baki d'aya bata tsaya kunnawaba sakata kawai tayi a jaka sannan tanufi 'kofar fita daga gidan.

Cikin sa'a taga gidan bud'e batayi wata-wataba tafito tad'au hanya dukda ba'kin duhun dake akwai ga unguwar tsit babu wani mahalu'ki bakajin motsin kome sai haushin karnuka da kukan tsun-tsaye.

Tafiya take batare datasan inda zataba, harta fito titi, nanma wani titi rami'ka batare datasan inda ze 6ulla da itaba.

Tun tana tafiya da sauran 'karfi-'karfinta har tafara gajiya tafara layi kamar wacce tasha tabugu.
Da-dai bakin wani junction taji an haske mata fuska da wata irin fitila me tsananin haske hannu tasa tana karewa muryar wani namiji taji yana cewa "hey your under arrest kune yan'iska masu shaye-shaye da yawon banza ko.

Kafin tayi wata mgana sunsakata mota sai ofishinsu.
Ganinta office d'in yansanda yasa hankalinta yad'an kwanta dan koba kome tasan ta ku6uta.







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------11


*washe Gari*  bayan sun dawo daga isalmiyyah, Hussaina taje d'akin Momy zaune ta isketa bakin gado tana nazarin wani littafin addu'oi cikin ladabi ta zauna kusa da ita.

"Momy wata Alfarma nazo nema gurinki, 
"Tame ina jinki fad'i, momy tace batare data kalletaba, 
Nan tashiga inda-inda tana ganin kamar 'karyar dazatayi bazata fishshetaba amma sai wata zuciyar tace "ki kwatanta hausawa sunce a rashin tayi akan bar araha.
"Dama Im...wai asibiti zamuje ganin mamar Zuby shine nakeso dan Allah ki taimakeni kibarni wlh namiki Al'kawarin bazan wuce awa d'ayaba.
"Kinga Hussaina banison abinda zezo yad'agamin hankali ina zamana lafiya, yanzu kije kisamu guri kiyi zamanki kuma mahaifinki yadawo yatarad bakinan wace amsa zanbashi,

"InshaAllah Momy bama zesan najeba, 
Haka dai tayita magiya har momy tabarta tare da saharad'in idan daddynsu yadawo bata dawoba zatace batasanma fitartaba, tace ta amince da hakan.

Cikin Zumud'i takoma d'akinsu ta d'auko wani tsadadden swiss less maroon colour tasanya sannan tasanya takalmi milk jaka milk, sai tayi too much kasancewar zaren da akayi kwalliyar less d'in milk ne sannan tabi da milk d'in mayafi, _{mashaAllah koni zee dana kalleta nasan ba 'karamin kyau tayiba}_

Hassana dake zaune tana bitar littafin ibadah wanda akayimasu 'kari yau, ta kalleta "uhm sister wannan gayu haka Kuma sai ina?
"Sorry sister sauri nakeyi idan nadawo zakiji,
"To Allah maidoki lafiya
"ameen kawai tace tafice, A falo ta tarad da momy saida gabanta yayi mummunan fad'uwa dan batayi tunanin ganinta nanba, 

Kallo Momy ta'karemata daga sama har 'kasa "keda zaki ganin marar lafiya kuma da wannan gayu haka, 
'Ka'karo murmushi tayi "Hmm Momy kuma dan za'a ganin marar lafiya ba'a sa kaya me kyau.
"To shikenan nidai nagayamaki karki dad'e.
"InshaAllah bazan dad'eba.

Tana fita tahau napep sai inda sukayi mahad'a da Hafiz, tana isa kuwa ta iskeshi a mota, bud'emata yayi tashige sannan suka d'au hanya.

Sunyi tafiya me nisa kafin su shiga rukunin wasu gidaje da Alama estate ne, bakin wani gida sukayi parking shine yafara fitowa sannan yabud'emata tafito tare suka jera har zuwa cikin gidan, 

Wani 'kawataccen falo yayimata masauki gidan tsit kamar ba mutane amma kuma yanayin kayan gidan zaka kallah kagane akwai mutane, zama sukayi suna fira sama-sama kusan minti sha biyar ba Alamar wani ze fito, nan Hussaina tad'an tsorata ta kalli Hafiz Wai ina mutanen gidanne, 
Murmushi yayi haba babyna kamar ba wayayyaba hajiya tana ciki yanzu zata fito, ina zuwa yafad'a tare da mi'kewa yanufi pridge lemun _5ali6e_ ya d'auko tare da cup d'in glass ya ajiyemata,
"Bari ingyama hajiya may be bataji shigowarmu bane, wani d'aki yashiga da Alama bedroom ne bayan minti biyar yafito ya kalli Hussaina wacce kallo d'aya zakayimata kagane a tsorace take "hajiya tana wankane amma tana zuwa, wai bakisha lemunba "Uhm na'koshi nidai sonike intafi gida kada amun fad'a kagafa har bakwai da minti sha tara tafad'a tana duba agogon wayarta.
"Koma miye ai kinsha koda lemunne kinsan idan bakishaba bazanji dad'iba.

Zubowa tayi cikin cup tad'an kur6a kad'an ta ajiye 
"Haba me kikasha nan?
Lemun yad'auka yacika cup d'in yafara bata da kanshi da ta'ki kar6a ganin ranshi ya 6aci yasa ta 'kar6a a hannunta ta shanye sannan ta ajiye cup d'in.

Cike da farinciki ya kalleta "kokefa babyna amma da kintsaya wani no'ke-no'ke "Uhm kawai tace dan tunda tasha lemun jikinta yamutu sai wata kasala data rufeta.

 Hafiz yana lura da halin datake ciki saboda haka mi'kewa yayi tare dayin hanyar d'akin dayashiga d'azu "ina zuwa nasan yanzu tagama.

Hussaina kuwa hamma tafara jerowa d'aya bayan d'aya tana lumshe idanu cikin minti bakwai bacci me nauyi yayi awon gaba da ita.

Saida ya dai-daici maganin dayazubamata a lemu ya Isa yin aikinsa sannan yafito ganinta yayi kwance kan kujera tana shara bacci wani shu'umin murmushi yayi tare da 'karasowa inda take.








Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------13


Wani d'an sandane ya kalleta Wanda da Alama shine babbansu yace "miye sunanki?
Jiki na kyarma tabashi amsa "Hussaina, 
"Ke yar gidan wacece kike yawo da wannan daren?
"Uhm wlh yalla6ai ba yawo nikeyiba, hasalima ni bansan ya'akayi nafito daga gidaba.
"Shut up, yafad'a cikin d'ga murya, ke muzaki rainama wayo, irinki-irinki mungamu yafi a 'kirga, hadama wad'anda sukafiki iskanci.
"waye zefitodake daga gidanku batare da izininkiba, kada kimanta cikin Halin da aka kamaki na maye koshima bakisan ya'akayi kikayi shaye-shayen ba?

"Wlh yalla6ai bansha komeba na rantsema da Allah, 
Tassss  saukar wani lafiyayyen mari taji a kumatunta wanda wannan d'an sandan ya d'auketa dashi, marinda saida ya gigitata saboda tsananin azabar tafin hannun d'an sandan ba 'karamin kato bane.

A 'kufule yace zaki fad'amana ke 'yar'waye kokuwa saina sa6amaki.
Cikin tsananin gigicewa take magana "zanfad'a.... Zanfad'a wlh.
"Oya ina saurarenki d'ansandan yafad'a tare da tsareta da manyan idanunsa masu ban tsoro.

"Ni Yar gidan Alhj Mansir company ce.
"What? 'Dan sandan yafad'a tare da mi'kewa tsaye.
"Karya kike yafad'a tare da nunata da yatsa, duk fad'in garinnan waye besan Alhj Mansir kamfaniba, mutumin kirki me halayya ta kwarai ace ke yarsace kina wannan munanan halaye.
Kuma ba wannan ba iya saninmu Alh Mansir bayada wasu 'ya'ya sai yara biyu yan tagwaye.
"Yan la6ai wlh nice ai mune yan tagwayen Nice Hussainar dan Allah Ku taimakeni Ku maidani gidanmu.

"Sajen Habu, dan sandan yakwalama wani daga cikin yansandan kira.
Da sauri d'ansandan ya iso gabanshi ya 'kame tare da saramashi.

"Maza a fiddo mota yanzu zamuje gidan Alh Mansir kamfani "yes sir yafad'a saida ya'kara saramashi kafin yafita zuwa ma'ajiyar motocin.

Dare ya tsala misalin 'karfe biyu na dare motar yan'sandan tayi parking bakin get din gidansu Hussaina, nocking sukayi lokacin mal bala yana kwance cikin d'an karamin d'akinsa yafito da sandarsa a hannu yana tamabayar "waye? Hussainace tayi magana "nice mal bala, "kece wah? Ya tambaya.
"Nice Hussaina.
"Husssaina da wannan daren subhanallah bud'e 'kofar yayi ahankali yana le'kowa yayi ido hud'u da ita da 'yansanda biyu tare da ita.

Da Sauri Hussaina tashiga gidan 'yansandan suka take mata baya, a harabar gidan suka tsaya "kishiga kiyimana magana da mahaifin naki.
Bata ko sauraresuba tayi cikin gidan da gudu,
Lokacin Daddy,Momy da Hussaina suna Zaune a falo, Momy sai Addu'a take Allah maidomata da 'ya lafiya a Zuciyarta tana cewa "danasan haka zata kasance daban amince da fitartaba.
Hassana kuwa kuka kawai takeyi, yayinda dady Zuciyarsa tagama 'konewa jiyake inama yaga Hussaina yanzu Allah kad'ai yasan irin dukan dazeyimata.

Begama wannan tunaninba yaga anturo 'kofar falon, mikewa yayi da sauri dan ganin me shigo masu gida da wannan tsohon daren, ido Hudu sukayi da Hussaina saurin isa yayi Inda take a zuciye ya dun'kule hannu yakaimata wani mugun naushi sannan yasa 'kafa ya hard'ota.
Fad'uwa tayi 'kasa tana maida numfashi sama-sama ko kukanma yakasa zuwamata saboda tsananin azabar datake ciki.

Dukda haka Daddy beyi 'kasa a gwiwaba gurin ciro cherger wata fitila dake jikin soket yarin'ka tsulamata, sai lokacin tasamu damar fasa ihu tare da d'aukewar numfashinta ta sulale 'kasa sumammiya.

Ganin tafad'i yasa Momy 'karasowa gurin tana kuka "innalillahi Alhj miye haka kake shirin kasheta, kabari mana kaji ta bakinta, "Bazanbariba da bata fitaba da hakan be faruba, kuma ko mutuwa tayi bani nadamar kasheta saboda da inyi mugun gani 'kara narasata baki d'aya.

Hassana kuwa ganin 'yar'uwarta kwance ba Alamar rai tattare da ita yasata rud'ewa tafito zuwa harabar gidan dagudu tana kuka, ganinta yasa 'yansanda sukayi saurin tarbarta a tunaninsu Hussainace saida suka kula da kayan jikin wannan basubane jikin wacce suka kawo yanzu "ke lafiya suka shiga tambayarta, a gigice take nunamasu cikin gidan tana cewa "daddy yakasheta, ya kashemin 'yar'uwa.
"What suka fad'a tare da abkawa cikin gidan baki d'ayansu..






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


Page-------------------------14


A gigice Momy tabi Hassana da kallo tare da 'yan'sandan dake tare da ita.
"Hassana Kina Haukane, mahaifin naki kika kirama 'yan sandan.
Cikin muryar kuka Hassana tace "Wlh momy bani nakirasuba ina fita nagansu a harabar gidannan.

Kallonsu daddy yayi a gadarance yace "waya kawoku gidana, kuma da izinin wah kuka shigo har nan? Yafad'a yana nuna inda suke tsai-tsaye.

"Babban cikinsune yayi magana "Sunana inspeter Sabi'u wale, mune wad'anda suka kawo wannan yarinyar gidannan bayan mun tsinceta cikin halin maye, bayan ta dawo hayyacinta mukayimata 'yan tambayoyi shine tasanar damu kaine mahaifinta shine muka kawota, muna tsaye a haraba munajiran tayimana magana dakai shine mukaga wannna tafito tana fad'in a taimaketa ankashemata 'yar'uwa shine dalilin dayasa muka shigo domin gudanar da aikinmu kamar yanda doka ta tanada.

"Owj naji duka bayaninku nagode, inaso kutafi kawai ni zan iya solving kowace matsala tagidana batare da wani yasamin hannuba nagode da taimakon dakukayima 'yata.

"Muma mungode Alhj Amma dan Allah ari'ka kai zuciya nesa, saboda gudun danasani....
Sai a hanzarta a kaita asibiti suka fad'a suna kallon Hussaina dake kwance bako motsi.


Bayan fitar 'yansandan momy ta kalle daddy Wanda yaketa mazurai da Alama har 'yanzu zuciyarsa bata gama hucewaba, 

Hussaina kuwa har 'yanzu tana kwance batasan inda kanta yakeba, momyce tamatso inda take ta tallabo kanta ganin ba alamar rai tattare da ita yasata fashewa da kuka, "Dan Allah Ahj mukaita asibiti kada tamutu.....

"Tamutun mana, yafad'a cikin d'aga murya.
Sannan yayi 'kasa da muryarshi yana cewa "ba inda zan kaita na kwammace inrasata baki d'aya da mugun halin datake Neman jefa kanta. 
Tajamani abin fad'i a gari, yana gama fad'in haka yashige d'akinshi ya maido 'kofa yarufe.

Cikin kuka Momy ta kalli Hassana tace kawomani ruwa.
Da sauri Hassana ta d'ebo ruwa cikin cup takawo, amsa Momy tayi tashiga kwarama Hussaina a jiki amma ko motsi batayiba saida ta zubamata a fuska sannan tayi firgigi ta tashi ta 'kan'kame Momy tana fad'in dan Allah kibashi ha'kuri wlh bazan 'karaba.

"Ke Hussaina kitsaya mana, ki nutsu nace ba daddynku bane nice Momy 
'Kara 'kan'kameta tayi tana fad'in "wayyo Momy wlh bazan 'karaba kigayamashi na tuba.

"Cikin tsawa Momy tace "dallah ni sakeni tare da tureta daga jikinta, kinsan kina tsoro kikaje yawon har kika kai wannan lokacin baki dawoba, itama tana gama fad'in haka tayi tafiyarta d'akinta tabar Hussaina nan tana kuka itada Hassana.

Hassanace tamatso kusada ita takama Hannunta ta mi'kar da ita tsaye suka nufi d'akinsu.
Koda suka shiga d"akin zaune sukayi jugum-jugum suduka suna sharar kwallah.

Ita Hassana tana kukan halinda 'yansandan nan suka fad'i sunkama Hussaina na maye.

Itakuma Hussaina tana kukan yaudara da Hafiz yayimata har yayi nasarar rabata da budurcinta.
Wasu sabbin hawaye suka zubo a kuncinta.

Hassana ta kalleta tare dasa hannunta ta sharemata hawaye 
"Dan Allah 'yar'uwata naro'keki ki gayamin gaskiyar inda kikaje har kikakai wannan lokacin baki dawo gidaba, kuma da gaskene abinda 'yansandan nan suka fad'i na kamaki dasukayi cikin halin maye? 

Tana gama fad'in haka ta tsareta da idanu tana jiran jin amsar dazatabata "Hmm ko d'aya Hassana wlh bansha komeba, kuma ni ba inda naje nasan dai naje asibiti kamar yanda na tambayi momy zanje kuma ta amincemin, ana gaf da magariba nabaro asibitin ina tsaye inajiran abin hawa wani me mota yatsaya gabana yaro'keni da inshiga yaragemin hanya nikuma ganin ina sauri yasa na Amince nashiga motar to shinefa daganan ban 'kara sanin abinda yafaruba saida na tsinci kaina yashe a titi, wannan shine gaskiyar abinda yafaru.

Hassana najin haka ta 'kara fashewa da kuka tare da rungume 'yar'uwarta tana fad'in "sister Allah yasa da rabon sauran shan ruwanki a duniya, ya Allah na godema daka kwatomin 'yar'uwata daga hannun muyagun mutane.

Hussaina kuwa dad'i taji har cikin ranta dan ganin Hassana ta yarda da 'karyar data tsaramata, a zuciyartama cewa tayi aiko gobe idan daddy da Momy sun tuhumeni abinda zan fad'amasu kenan, da haka suka kwanta bacci yayi awon gaba dasu kowace da tunani barkatai a zuciyarta.


          *Washe Gari.*

Koda suka tashi bayan sunyi duk abinda yadace na gyaran gida, komawa sukayi d'aki sukayi wanka wasu dogayen riguna suka sanya masu kyan gaske tare da 'yan 'kananan hijab.

Lokacin Momy tagama had'a break fast zuna zaune kan dining tana zubama daddy kasancewar tara hartayi yana sauri yafita office saboda yanada ayyuka da dama a can.

Jerawa sukayi gwanin ban sha'awa suka nufi inda iyayen nasu suke sannan suka zazzuna bayan sun gaishe da iyayen nasu.
Hussaina sai sunne kai takeyi alamar rashin gaskiya.

Bayan sunkammala breakfast ne daddy ya kalli Hussaina tare da d'dd'aure fuska kamar beta6a dariyaba yace "inaso kigayamin gidan ubanwa kikaje jiya.

"Uh...im asibiti naje ganin mamar 'kawata.
"Da izinin wah kika fita?
Kallon Momy tayi suna had'a ido Momy ta watsamata wata muguwar harara, ba shiri ta saddar da kanta 'kasa, tayi shiru.

Dadyne yacigaba da magana "koma waye ya d'aure maki gindi a gidannan kike Neman lalacewa tonidai ba agabana ba, kuma yau basai gobeba zan d'auki mataki kanki dan bazan zauna ina kallonki kijamin surutu a gariba, yana gama fad'in haka ya d'auki jakarsa yafice daga gidan ranshi a matu'kar 6ace.











Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป
[1/2, 8:33 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................15


Daddy ne Zaune office d'insa yahad'a hannu bibbiyu ya buga tagumi ba abinda yake tunani sai irin rayuwar da Hussaina take neman jefa kanta, 

Mi'kewa yayi tsaye ya maida hannuwansa duka biyu baya tare da fara zagaya office d'in  yafara zancen zuci "yanzu wane mataki yakamata in d'auka dan ganin nayima tufakar hanci bata war-wareba, yau kimanin shekara ishirin ina tarbiyantar da yarannan amma lokaci d'aya suna nema su bijiremin, komawa yayi kan kujera ya zauna tare da maida kanshi sama ba abinda yake tunani sai abinda 'yan sandan dasuka kawo Hussaina gida suka fad'i na cewa sun kamata cikin Halin maye, wato rayuwar dazata jefa kanta kenan, wadda daga haka mutum ze iya aikata kome hatta da kisan kai mashayi na iya aikatawa batare da shakka ko shayin irin hukuncin daze biyo bayaba.

"Assalamu Alikum, da sallama jabeer yashigo office d'in hannunsa d'auke da wasu files-files, jin shiru ba'a amsa sallamar ba yasa ya'kara yin wani sallamar karo na biyu, nanma shiru daddy be amsaba dan yayi nisa cikin tunanin dayake, guri jabeer yasamu ya zauna tare da ajiye files-files d'in kan tebur d'indake gabanshi da d'an 'karfi yanda daddy zeji karar ajiyewar. Hakan kuwa ya maidoshi daga dogon tunanin dayake ya d'ago da kanshi ya kalli jabeer "Ah jabeer badai har kagamaba, "eh nagama gashinan saura wad'annan files d'inne sunada 'yar matsala akwai takardun da babu aciki, yafad'a yana ware wasu files guda biyu gefe.

"Owk to ba Matsala idan na duba zanyima magana sai a gyara, "to kawai yafad'a tare da mi'kewa ze fita daga office d'in harya kai bakin 'kofa daddy yayi kiransa "jabeer, cikin girmamawa jabeer ya amsa tare da dawowa ya zauna, 

Saida daddy yayi shiru na kimanin minti biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya "Jabeer dama inason magana dakai "to Alhj Allah sa dai lafiya, 
"Eh to lafiya lao, kan maganar Aurenka da Hussaina kanasonta kuwa har yanzu?
Cike da jin kunyar tambayar da daddy yayimasa ya amsa da "eh.

"To bakada matsala inaso da anjima bayan sallar azahar kataho da magabatanka da shedu koda basu wuce mutum gomaba, nima zan sananar da 'yan'uwana za'a d'aura aurenku kaida ita, bani bukatar kome naka sadaki kawai zaka taho dashi naira dubu hamsin, 
Kada kayi mamaki kan wannan abin dana aiwatar akwai dalilin yin hakan Wanda nasan koda kaji dalilin na tabbata bazaka'ki jininaba, 

Jabeer dai shiru yayi yana sauraron Alhj cike da mamaki a zuciyarshi yana cewa "wannan shine ikon Allah me tsaida wando koba zariya,  kome wannnagaggawar take nufi Allahu wa'alamu.

Haka ya kauda kowane tunani cikin zuciayrshi yayima daddy godiya sannan yakoma office d'inshi.
Koda ya koma tunanin dai yahanashi sukuni saboda haka rufe nashi office d'in yayi Yakama hanyar gida.

         *Waye Jabeer*

Jabeer Suleman shine asalin sunanshi Haifaffen garin katsina, Alh sule tankuri shine mahaifinsa sai mahaifiyarsa Hajiya sa'ada sunada rufin asiri Bakin gwargwado amma ba'a kiransu masu arziki, su biyu iyayensu suka haifa dagashi sai 'kanwarsa Nusaiba wacce akwai tazara sosai tsakaninsu dan ahalin yanzu nusaiba bata wuce shekara sha shidda zuwa sha bakwaiba yayinda jabeer yakeda talatin da d'aya.
Tun yana d'an shekara sha bakwai mahaifinsu yarasu lokacin mahaifiyarsu na d'auke da 'karamin cikin nusaiba bayan rasuwar mahaifinsu da wata bakwai ta haifi nusaiba, haka sukacigaba da rayuwa yau da dad'i gobe babu, yayinda mahaifiyarsu ta tsaya tsayin daka dan ganin jabeer yayi karatu, da kyar da sud'in goshi sukasamu ya kammala karatunshi a F.C.Ekatsina kasancewarshi hazi'ki yasa yasamu sakamako me kyau amma dukda haka samun aiki yayi wahala kusan shekara biyu yana neman aiki besamuba, kwatsam rannan yaji ana Neman ma'aikata a Company Alhj mansir badan yasa ran zesamuba yaje yayi interview cikin ikon Allah kuwa  saiga sunanshi cikin wad'anda aka d'auka aiki, sunyi matu'kar farinciki shida mahaifiyarshi da 'kanwarshi, ranar dazefara zuwa aiki mahaifiyarshi tayimashi nasiha me ratsa jiki akan ri'kon amana da gaskiya, sannan tabishi da addu'ar samun s'a.

Bayan wata shidda dafara aikinsa Alhj mansir yalura da Halin gaskiya da ri'kon amana na jabeer hakan yasa yajawoshi jiki tare da 'karamashi matsayi a office d'in Wanda a halin yanzu shine mataimakin manager company.



*Masu yimin magana ta prvt najina dasukayi shiru kwana biyu Dan Allah kuyi hakuri na rashin ganin reply d'ina naga sa'konku saidai be karantuwa kasancewar nasake download whatapp ne nagode da kulawarku.*




Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป   shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀
[1/4, 7:48 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................16
 

Saboda haka cike da tunani barkatai jabeer ya isa gidansu, 'kanwarsa Nusaiba yafara gani zaune falo tana kallon wani Indian film me suna salam namaste, da sauri ta tarbeshi tanamashi sannu da zuwa, bayan ya amsa d'akinsa yanufa ya ajiye jakarsa sannan ya dawo falon, har yanzu dai nusaibar ce ita kadai a falo tambayarta yayi "ina mama?
"Tana bedroom,
"Owk kawai yafad'a tare da nufar 'kofar dazata sadashi da d'akin kwanan mahaifiyar tashi, da sallama yashiga d'akin zaune ya isketa gefen gado hannunta ri'ke da waya da Alama waya tagama, kallonshi tayi bayan yasamu guri ya zauna kan bedsite "a'a jabeer yanaganka kadawo tun yanzu ko mantuwa kayine?
"A'a mama ba mantuwa nayiba wani babban Al'amari ya maidoni Wanda ni kaina ya d'auremin kai,

"Wannan wane Al'amarine tafad'a tare da maida duka hankalinta gareshi, 
"Watako yanzu danaje office shine Alhj yakirani yake cemin inje insanarda magabatana kuma inbada kud'in sadaki naira dubu hamsin yau ze d'aura aurenmu da Hussaina.

"Alhamdulillahi mama tafad'a tare da d'aga hannuwanta sama tana godema Allah, kai Amma naji dad'i wannan abu ai abun farincikine dama kullum Addu'ata be wuce inga aurenkaba, Allah sanya Alkhairi yabaku zaman lafiya.

"To amma mama kina ganin babu wata matsala, "wace matsala haba jabeer me kanema karasa inaji kadade da kammala gidanka, kuma Hallacin da Alhj mansir kamfani yayimana ai kobakada kome yace ka auri d'iyarsa ka aureta kazubama sarautar Allah ido dan nasan baze barka hakaba,
"To mama Allah dai yasa haka shine mafi alkahiri,
"Ameen haka nikeso naji kana fad'i.
Daga nan yafita zuwa d'akinshi ya canja kaya sannan yakoma yayima mamarsa sallama tare da sanar da ita zeje ya d'auko mutum ukku dangin babanshi sannan mutum ukku a dangingin ita mamar tashi, fatan Alkhairi tayimashi sannan yafita.

         ⏱. *Misalin 'karfe 3:00pm*


Aka taru a masaalacin dake 'kofar gidan Alhj mansir mutane 'kalilan suka sheda d'aurin auren Jabeer Suleiman tankuri da Amaryarsa Hussaina Mansir kamfani, bisa sadaki dubu hamsin.

Bayan ankammala Alhj mansir yasa aka gabatarma duk mutanen dasuka halarci d'aurin auren abun lasawa take away akayima akaiyma kowane suka wuce suna sanya Albarka.

 Bayan ankammala wannan daddy yashiga gida da sallama, su duka falo ya taraddasu zaune Momy ce ta amsa sallamar, Hassana tace "daddy sanu da dawowa "yauwa ya amsa,
Hussaina kuwa daddy nashigowa jikinta yafara kyarma dan wani masifaffen tsoronshi takeyi, cikin muryar tsoro tace "d...dad...daddy sannu da zuwa.
Wani matsiaycin kallo ya watsamata sannan yawuce d'akinsa batare daya amsa sannu d'inda tayimashiba.

Can bayan kimanin minti baiyar yafito ya kalli Hussaina "ki shirya yanzu inaso zan fita dake kuma minti talatin nabaki, kinajina "inaji daddy tafad'a tare da mi'kewa tanufi d'akinsu jiki na kyarma.

Daddy kuwa fita yayi harabar gidan, waya yakira jabeer "ya masu aikinnan sun kammala kuwa,? Ya tambaya 
cikin ladabi jabeer yake magana "Eh Alh sunyi kusan minti sha biyar ma da gamawa.
"Sun had'a kome dai yanda yakamata ko?
"Eh sun had'a kome 2 bedroom ne da falo 2 sai kitchen ba abinda ba'a zubaba na bu'kata.

"Owk to anjima ka shiryar tarbar Amaryarka,
Kasa magana jabeer yayi saboda kunyar Alhj yakeji sosai.

"Basu dad'e da kammala wayaba wata had'addiyar mota tayi parking 'kofar gidan sannan wasu maza suka ri'ka jido akwatina suna shigowa dasu saida suka shiga da guda goma manya- manya, sannan sukayima jabeer bayani Alhj mansir yace akawo kayan amaryane.
Mamakine yahana jabeer magana danshi harga Allah yayi niyyar had'a wannan kayan Amma Alhj yahashi had'a kome.







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀
[1/5, 8:31 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................17



 Da misalin 'karfe biyar na yamma Hussaina tafito cikin shiri sanye take da riga da zani d'inkin simple atamfar brown colour haka takalmin 'kafarta yayi kala da kayan jikinta sai 'katuwar hijab data sanya, ahankali take takowa hartazo gaban dadynsu cikin ladabi tace "na shirya daddy
"Owk muje ko, yafad'a yana nunamata 'Kofa.
Ganin tana tafiya Ahankali kamar kazar da Kwai yafashemawa a ciki yasa daddy yayi gaba ya zauna a mota yana jiran fitowarta.

Fanin fitarsa yaba Hussaina damar yin magana "Momy wai ina zamu? 
Momy tace "kin tambayi kaza hanyar rafi.....
Ni kaina da kike gani bansan meke wakanaba nidai kawai abinda nasani naga tunda Alhj yatashi yau yaketa hidima ko zama yaci abinci beyiba.

Hassana dake zaune tace Allah dai yasa Alkhairi ne, ni kaina ina mamakin yanda daddy yace Hussaina ta shirya su fita batare daniba, Alhalin nasan ko'ina tare muke zuwa.

Momy tace "to wannan abu dai Allah kad'ai yasani, kiyi sauri kibishi kada kuma yaga kin 6atamai lokaci.
Juyawa tayi tafita daga falon batare data 'karayin wata maganaba.

A mota ta iske daddy zaune yana jiran fitowarta, gidan gaba tanufa da niyyar tashiga harta kama murfin motar zata bud'e daddy ya watsamata wani matsiyacin kallo "koma baya.
Jiki na 'kyarma takoma ta bud'e bayan motar tashige, sannan daddy yatayar da motar Malam bala yabud'emasu get yana d'aga masu hannu suka d'au hanya sannan yamaida get d'in yarufe Yakoma kan d'an bencinsa ya zauna yana cewa "gaskiya Alhj ya iya maganin d'an iska, wato yarinyar nan wlh da Alhj beyi saurin Aurar da itaba saita d'aukomar abin kunya. Kodayake bansaniba shin itace koba itabace oho nikam bani ganesu, radio shi yajawo ya kunna yacigaba da sauraron abinshi.

Daddy kuwa ba inda ya zarce da Hussaina sai unguwar dutsin safe malali Quarter's inda nan tangamemen gidan jabeer yake, bakin get yayi horn da sauri megadi ya bud'e mashi ciki yashiga ya ajiye motarshi inda aka tanada dan ajiye motocin, fitowa yayi sannan ya umarci Hussaina data fito itama, ba musu tafito tunda suka shigo take yaba kyan gidan, saikuma yanzu ta'kara ganinshi sosai tsarin gidan ya burgeta, a zuciyarta tace "nan kuma ko gidan waye? Amma ko gidan abokanin daddy ne bamu ta6a zuwaba, kuma sabodame daddy yaza6i yazo dani ni kad'ai banda Hassana Alhalin duk inda zamu tare muke tafiya da ita......

Daddyne ya tsinkemata tunanin datake ta hanyar cewa "shigo mana.
Ba musu tabi bayanshi wata 'Kofa yabud'e wacce tasadasu da babban falon gidan me d'auke da maka-makan kujeru irinna zamani a tsakiyar falon gefe kuma kan wani step kujerun dining ne da 'katon table d'insu, daga gaba kuma inda suke facing wata 'katuwar TV ce plasma ma'kale jikin bangon sai manyan speaker's (Home theaters) gefensu kuma wasu kyawawan flower's ne masu d'aukar ido, duka kayan falon sun kasance purple colour hatta da pentin d'akin kalarsa kenan, 

Daddy yace "to Hussaina wannan gidan da kike gani bana kowa bane face gidan mijinki......
Dammmm gabanta yayi wani mummunan fad'uwa da sauri tad'ago ta kalli daddy ganin ba wasa tattare dashi yasa tamaida kanta 'kasa gabanta nacigaba da fad'uwa.

Daddy yacigaba da magana "naza6i na aurar dake dakijawomin abin kunya, saboda nan shine gidan aurenki, ki zauna kibi mijinki kiyi mashi biyayya Aljannarki tana 'kar-kashin tafin 'kafarsa idan kinbishi kisamu idan kuma kin baud'e wannan kuma Allah yasan hukuncin daya tanadar maki.
Saboda haka iname umartarki daki zama me biyayya a gareni ni mahaifinki dakuma mijinki ki zauna lafiya.

Nan daddy yayimata nasiha me ratsa jiki kafin yayimata bankwana ya ajiyemata bandir d'in kud'i yan dubu yace "saboda idan kina bu'katar wani abu bance ki matsama mijinkiba, 
Bayan tafiyar daddy kasa tashi tayi daga inda yabarta, tunani take "wannan wane irin aurene daddy yayimin kamar auren wasa, to wai yaushema aka d'aura auren? Kuma waye mijin? Ina daddy yasamu mijin daya yarda da aure cikin kwana d'aya tak? Haka tagama jerama kanta tambayoyi amma batada amsarsu kuma batada Wanda ze amsa mata, hakan yasa tafashe da wani irin kuka, tana cewa "shikenan yanzu nasan daddy baya 'kaunata menayi....menayi daza'a yankemin wannan hukuncin.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀
[1/7, 10:28 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................18



Kuka take iya 'karfinta babu me rarrashinta sai da tayi me isarta sannan ta tashi falo na biyu tashiga wanda shima yaji set d'in kujeru da kayan kallo amma sai dai shi bekai na farkon haduwaba shikuma kome nacikinsa green colour ne, tsayawa tayi ta'karemashi kallo sannan tanufi wani d'akin nan kuma bedroom ne wanda aka zubama kaya yan Dubai ba 'karamin kyau d'akin yayiba, fitowa tayi daga nan tanufi gudan d'akin ahanakali tatura 'kofar tashiga nan ma karo tayi da wani 'kawataccen d'akin kwana shikuma duka kayan yan Nigeria ne aka zuba amma harma sunso Sufi na Dubai d'in kyau.

Bayan tabi ko'ina na gidan ta'karemar kallo dawowa tayi a bedroom ta zauna tsakiyar gadon tare da rufe fuskarta da hijab d'inta, take tunanin Hafiz ya dirar mata a zuciya, wani irin kuka tafashe dashi a zuciyarta tana cewa "yanzu shikenan anrabani da Hafiz mutumin danafi so nafi 'kauna akan kowane namiji, bazan iya zaman aure da kowane namiji ba bayan Hafiz yazanyi da rayuwata, haka tacigaba da kuka tana zancen zuci.

"Yanzu ni waye wanda daddy yaza6amin anya zan iya zama dashi, ita ko kad'an bata kawoma ranta jabeer ne wanda aka d'aura mata auren dashiba.

Zaune take tabuga uban tagumi hannu bibbiyu ba abinda ke mata yawo a kwalwa sai kalar salon soyayyar da Hafiz ke nunamata, yanzu shikenan anrabamu baze 'kara shayar dani zumar 'kaunarsaba.

Mi'kewa tayi tsaye kamar wacce aka tsikara "baze yiyuba tafad'a a zahiri bazan iya rabuwa bada Hafiz ba ko ana ha maza ha mata, Hafiz shi kad'aine namijin dazan aura in kasance cikin farin ciki, ko waye wannan yayi gan-ganci daya yarda da aurena, tabbass zesan abinda ya auro ya kawo gidanshi.

********

Momy da Hassana kuwa tun bayan fitar daddy da Hussaina suketa sa'ke-sa'ke da kwancewa sun rasa ina daddy zashi da Hussaina batare da yar'uwartaba Alhalin shine yasaba masu da duk inda zasu tare suke tafiya.

Da sallama ya shigo falon suduka binshi sukayi da ido ganin yadawo batare da Hussaina ba, 
Momy ce tayi 'karfin halin tambayarsa "Alhj ina Hussaina take naga ka dawo kai d'aya kuma bayan tare kuka fita.

"Tana gidan mijinta, yabata amsa a takaice sannan yawuce d'akinsa, binshi tayi daga baya zuciyarta cike da mamaki.

Hassana dake zaune tanajin abinda daddy yafad'a itama tashi tayi tanufi d'akinsu tana cewa "innalillahi wa'innalaihirraji'un "Gidan miji.... tafad'a cike da mamaki, yaushe aka  d'aura auren sister bamu saniba dan gashi alamu sun nuna itama momy batasan da zancen ba,
"Ya salam tafad'a tare da dafe kanta da hannu biyu dataji yana saramata kamar ze rabe biyu, fad'awa tayi kan gado tana zubar da hawaye.


: Cike da 6acin rai momy take magana "haba Alhj ban fahimce inda zancenka yadosaba.

Juyowa daddy yayi ya kalleta tare da yin wani murmushi, sannan yace "baki bu'katar in maimaita maki abunda nafad'a d'azu saboda inada tabbacin kinji kome nafad'a.

"Lalai Alhj yanzu ka tabbatar min da baka 'kaunar Hussaina akan me zakayimata irin wannan hukuncin, aure cikin kwana biyu kamar auren d'iyar kara, haba Alhj kuma amatsayina na mahaifiyarta yaci ace nasan da maganar amma bansaniba kuma banida labari kawai saika tafi da yarinya kace wai wani ka kaita gidan miji, gaskiya ni ban yardaba kawai kafad'amin inda d'iyata take inje in d'aukota idan kai baka sonta ni ina sonta, duk wannan maganganun da momy keyi tanayinsune cikin 6acin rai da d'aga murya. 

"Dakata Maryam, daddy yafad'a cikin d'ga murya "wannan auren na d'aurashi kuma yariga ya d'auru ba wanda ya isa ya war-wareshi, ince idan yarinyar nan ta jawo mana abin kunya zagin daza'ayimin baza'ayimaki rabinshiba, saboda haka nariga na yanke hukunci idan kinji hukuncin danayimaki bemakiba zaki iya kama gabanki hanya a bud'e take yara kuma nawane inada iko akansu.

Tunda daddy yafara fad'a momy ke kallonsa cike da mamaki a zuciyarta tace "lallai Alhj da gaske yake kuma ba wasa tattare dashi dole nima inbi ahankali.

Cikin langa6ar da kai momy tamatso kusa da daddy ta dur'kusa gabansa "Haba Alhj meyakai na 6acin rai haka, indai kan wannan maganar ne inshaAllah kome ya wuce Allah sa haka shine mafi Alkhairi a rayuwar Hussaina, itakuma yar'uwarta Allah kawomata miji na gari.
"Ameen daddy ya amsa tare da shigewa toilet ya watsa ruwa sannan ya d'auro Al'walar magrib dan lokacin sallar yayi.
Itama Momy d'akinta tanufa ta d'aura Al'wala ta kabbara sallah bayan tagama ta dad'e kan abin sallar tana kwararo addu'a ga yaranta.





Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป  shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ”ซ
[1/8, 9:50 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................19



Zaune take cikin d'akin tarasa mekemata dad'i a duniya, wayarta ta Dauko sunan zuby ta lalubo sannan ta danna kira, bugu d'aya zuby ta d'auka.
"Hellow 'kawata kin 6oye kwana biyu.
"Hmm kedai bari kawai zuby idan ana sallah ba'a magana.
"Banganeba 'kawata wani abune yafaru dake?
"Abubuwa da dama sun faru dan ahalin yanzu wayar nan damuke dake ina gidana.
Saurin tashi zaune zuby tayi daga kwancen datake "bangane gidankiba 'kawata, gidanki ko gidanku?
"Hmm gidana dai dan daddy yamin aure kuma yau natare.
"Aure kuma Hussaina, to waye angon zuby ta tambaya gabanta na dukan ukku-ukku kada Hussaina tacemata Hafiz ta aura, idan ko haka ta kasance da ba abinda ze hana abkuwar 'karamin ya'ki tsakaninta da Hussainar.
Hussainar ce tadawo da ita daga duniyar tunanin data lula, 
"Wlh nima har yanzu bansan ko waye mijin ba, amma inaso kizo gobe, 
"To shikenan 'kawata zanzo amma wane unguwane?
Nan Hussaina tabata full address sannan sukayi sallama kowanensu ya tsinke wayar.

Zuby kuwa tashiga tsananin rud'ani, tashi tayi tsaye tafara kai komo cikin d'akin "tabbass idan har tunanina ya tabbata Hussaina Hafiz ta aura tofa sainayi yanda nayi narabasu koda kuwa ta Hanyar salwantar da rayuwartane, inason Hafiz ina 'kaunarsa bazan juri ganinshi tare da wata maceba bayan ni, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge,sannan tanufi lokar dake jikin gadon d'akin tasa hannu ta fiddo kwalbar kodin ta tuttule a bakinta ta shanye sannan tafad'a gado tana mayarda numfashi kafin bacci yayi awon gaba da ita.


: Hussaina kuwa cigaba tayi da bin d'akin da kallo kad'an-kad'an takai dubanta ga 'Kofa tana jiran ganin shigowar angon nata.

Ringing d'in wayarta tajiyo da sauri tasa Hannu ta d'auka dan tana tunanin zuby ce takirata kozata gayamata wani abu amma sai ganin sunan Hafiz tayi 6aro-6aro yana yawo kan screen d'in Wayar, sai da gabanta yayi mummunan fad'uwa bin wayar tayi da kallo har kiran ya tsinke sake kira akayi karo na biyu nanma batayi gigin d'aukaba dan ganin kiransa kayar mata da gaba yakeyi, duk dahaka beha'kuraba ya'kara kira karo na ukku hannunta na rawa ta daure ta danna OK tare da karawa a kunnenta batayi maganaba sai shi yafara magana.
"Hellow babyna kina lafiya?
Shiru tayi duk illahirin jikinta kyarma yake dan jin muryar Hafiz kad'ai jefata yake cikin wani yanayi me wuyar fassarawa.
Magana ya'karayi karo na biyu "hello babyna ko bakyajinane.
Sannan ta daure murya can 'kasa-'kasa tace "ina jinka.
"Amma kuma kikamin shiru, kinsan kuwa yanda nadamu dake, kinsan halin dana fad'a na rashinki danayi kwana biyu......

Cikin d'aga murya da masifa Hussaina tafara magana "dakata Hafiz bakada wani dad'in baki dazakayimin bayan ka cuceni ka cuci rayuwata karabani da abinda duk wata mace take ta'kama da tin'kaho dashi a duniya.
Amma bakome ba laifinka bane laifinane dana d'auki yardata nami'ka maka d'ari bisa d'ari, gashi yanzu ina gidan mijina banida wata daraja da 'kimar daze kalleni da ita.

Dakata Hussaina nifa bangane inda maganganunki suka dosaba, 
"Tunda ka yaudareni ka kaini gidanka da sunan zan gaisheda hajiyarka ashe da wata manufar ka kaini danka ketamin haddi.......

Jitayi ana doka sallama daga falo hakan yasa tayi saurin kashe wayar baki d'aya ta turata 'kar'kashin filo, sannan tayi saurin janyo hijab d'inta tarufe fuskarta dashi.

Jitayi annufo d'akin datake hakan yasa fad'uwar gabanta ya yawaita, 
"Assalamu Alaikum warahamatullah, yafad'a tare da 'karasowa cikin d'akin ya zauna bakin gado.
Koda jin muryar kunnenta ya tabbatar mata da tasan me wannan muryar jin 'kamshin turarensa yadaki hancinta ya'kara tabbatarmata datasan kowaye,
Saurin bud'e lullu6in datayima fuskarta tayi dan tabbatarma idanunta abinda take tunani.
Tana bud'ewa kuwa sukayi ido hud'u da jabeer, a firgice ta nunashi da hannunta tana fad'in "Jabeer dama Kaine mutumin dayaimin yankan 'kauna, karabani da Wanda nakeso, kasa daddy yayimin aure irinnan d'iyar wasan yara aure cikin kwana biyu, bayan nadad'e da sanar maka inada wanda nakeso bakaiba, to ina me tabbatarma saikayi danasanin aurena dakayi, idan kayine dan farincikin rayuwarka nikuma ka ba'kantamin rayuwa to wallahi kaima ze zama ba'kin ciki a gareka.

"Haba hussaina banyi haka dan in ba'kantamikiba, kuma da banisonki bazan aurekiba inaso ki d'auki wannan a matsayin 'kaddarace agaremu kuma muyi fatan Allah sa tazamar mana Alkhairi a rayuwarmu.

Wani irin kuka tafashe dashi dan tunawa datayi batadafa wata daraja da 'kimar da sauran mata keda ita barantana tayima jabeer wula'kancin dataga dama abinda yafi kawai tabada kai bori ya hau, sannan tayi biyayya ta zauna lafiya ko Allah zesa yarufamata asiri, goge hawayenta tayi tace "to Allah shigemana gaba kuma Allah tabbatar mana da Alkhairi cikin wannan zama namu.
Jabeer ya Amsa da Ameen har cikin ranshi yaji dad'i da kuma mamakin saukowar Hussaina haka.







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ™Š
[1/8, 8:40 PM] Zee Elkaseem: [08/01 8:15 pm] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................20


Daga nan ya umarceta dasu gabatar da sallah su godema Allah kamar yanda addini ya tanada, ba musu tanufi toilet ta d'auro Alwala sannan shima ya Shiga ya d'auro tasa Alwalar suka gabatar da sallar nafila, bayan sun kammala ya dad'e yana kwararo masu addu'oi kafin su shafa.

Sannan ya d'auko ledar daya shigo da ita ya ajiye tsakiyar carpet d'in dake malale a bedroom d'in, da kanshi yanufi kitchen ya d'auko masu palate da cup, gasashiyar kazace guda ukku yabaje kan tire tare da fresh milk da lemun 5alive.

Juyowa yayi ya kalli Hussaina wacce take takure duk tabi ta raina gaskiyarta binshi kawai take da kallo, a zuciyarta kuwa tunanin abinda ze biyo baya takeyi bayan Jabeer ya kusanceta yajita ba cikakkiyar budurwaba, wasu guntayen hawaye suka zubo a idonta tayi saurin sa bayan hannunta ta goge batare da jebeer d'in ya luraba.

 Jabeer d'inne ya maidota daga dogon tunanin datake ta hanyar matsowa kusa da ita "bismillah gimbiya saurautar mata nasan dai kinajin yunwa yakamata ace kinci wani abu kafin ki kwanta.

Kad'a kai tayi kamar 'kadangaruwa "a'a ni banajin yunwa.
"Ban yardaba gaskiya da ganin wannan cikin ya dad'e rabonsa da abinci, yafad'a tare dakai hannunsa kan cikinta.
Ture hannun nashi tayi "nifa banajin yunwa, 
"To naji bakijin yunwa amma ban yarda ki 'ki cin komeba, kawai dai inajin sarautar takice ta motsa, uwar gida sarautar mata, yafad'a cikin tsokana.

Hannu yasa ya yago naman yanufi bakinta dashi da niyyar yabata tayi saurin kauda kanta, 
"Haba Hussaina bekamata ace kin'ki kar6ar komeba idan kikayi haka nikam bazanji dad'iba, dan Allah badanniba ki taimakamin ki kar6a.

A hankali ta juyo yafara bata abaki saida ya tabbatar data 'koshi sannan yazubo fresh milk nanma da kyar ta shanye cup d'aya.

Shima sama-sama yaci naman kajin sannan yakora da lemu, d'akinsa yanufa yacire kayan jikinsa yafad'a toilet yashe'ka wanka.

Hussaina kuwa tana ganin fitarshi tanufi wadrope tana bud'ewa taganta ma'kare da kaya, batayi mamakiba dan daddy yafad'amata babu abinda ba'a tanadar mata a gidan ba.

 Wata fitinanniyar rigar bacci ta d'auko wacce zamu iya kira akwai ya babu, ta sanya sannan tabi duk illahirin jikinta ta feshi da sassayan turare, sannan tabi lafiyar gado tayi kwanciyarta batare data rage Hasken d'akinba kuma tayi hakane dan tanajin tsoro ganitake kamar idan ta kwanta a duhu-duhu wani abu ze sameta tasaba kullum tanajin motsin Hassana kusa da ita, yau gashi zatayi kwanan kad'aici dan taga Alamar Jabeer banan ze kwanaba tunda gashi yatafi gudan d'akin yabarta, da wannan tunanin bacci 6arowa yayi awon gaba da ita. 

Sanye yake da best da short niker, farare 'kal jikinshi sai tashin 'kamshin turarensa yake me suna *story of love* yanufi d'akin.

Ganin d'akin da haske ya tabbatar mai da Hussaina batayi bacciba, da sallama yashiga jin bata amsaba yasashi dubawa kobata d'akinne, can ya hangota kwance kan lafiyayyen gadonta tanata sharar bacci hankalinta kwance, karsa shiga yayi cikin d'akin sannan ya maida 'kofar yarufe, kafin ya isa gareta ya'karemata kallo, yanda rigar baccin jikinta take sharara ba abinda be bayyanaba na surar jikinta, take yaji wata matsananciyar sha'awarta ta kamashi rage Hasken d'akin yayi tare da kunna masu fitila me sau'kin haske, ya haye gadon ya rungumota gaba d'aya jikinsa.










Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป Shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀⛄
[1/9, 8:14 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................21



A hankali yafara shafa lallausar fatar jikinta, yayinda ya tsinci kanshi cikin wani irin farin ciki marar misaltuwa.
Can cikin bacci Hussaina taji Alamar mutum kusa da ita ahankali ta bud'e idonta, tozali tayi da jabeer Wanda ya lula cikin duniyar 'kaunarta yana aikamata da sa'konni soyayya masu wuyar fassarawa, wani irin dad'i taji cikin ranta wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba, 'kara shigewa tayi jikinsa tare da sakar mashi duk wani sashe na jikinta, shikuma yacigaba da sarrafata da kwarewarsa da gogewarsa, Hussaina kuwa mamakin jabeer ne yacikamata zuciya "wai dama haka jabeer ya iya soyayya ya iya salo daban-daban amma lokacin kafin suyi aure yake nunamata shi ustaz ne kullum beda magana sai wa'azi da nasiha.
Da wannan tunanin kawai ta ida mallakamashi kanta, a daren sukasha amarcinsu ranar jabeer yasan Hussaina mace, kuma ba 'karamin farin ciki yayiba na yanda ya sameta cikakkiyar budurwa.

Hussaina kuwa banda kuka babu abinda takeyi saboda zafi da rad'ad'in datakeji, jabeer kuwa rarrashinta yari'kayi, dan wani sabon shau'kin sontane ya'kara kamashi.

Tashi yayi yanufi toilet yayi wanka ya tsarkake jikinsa, sannan yahad'a wani ruwa me d'umi ya dawo ya d'auki Hussaina yanufi toilet d'in da ita, zaunar da ita yayi cikin ruwan dan tad'an gasa jikinta, sannan yafito ya gyara gadon tare da canja masu bedsheets, bayan yagama yakoma toilet d'in lokacin Hussaina tagama wankan zuwa yayi da niyyar ya d'aukota amma saita kauce ta ma'kale kafad'a bataso, be matsamataba tunda ta nuna bataso hannunta yakama suka fito tana taku ahankali, kan gado ya taimaka mata ta kwanta sannan ya 'kuremata a.c d'akin kasancewar lokacin ana zafi.

Komawa yayi toilet ya d'auro wata sabuwar Al'wala sannan yazo ya kabbara sallah, nafila yari'ka jerowa saida yafarajin bacci sannan ya sallame ya dad'e yana kwararo addu'a kafin ya shafa, sannan Yakoma kan gado ya kwanta ya rungome matarshi yanajin wani sabon sonta da 'kaunarta na 'kara kamashi, a zuciyarshi yace "Allah kenan da yanzu bani bane angon dazesha amarci wannan daren yanda Hussaina tanuna tsana da tsangwama agareni batare danayimata wani laifiba, dayake Allah ya nufa nine mijinta yau gata jikina kwance numfashina na gauraya da nata, Allah nagodema....

Da wannan tunanin bacci 6arawo yayi awon gaba dashi.
_{Nikuma Zee danike biye dasu ina kwaso maku labari nace asuba ta gari, *Oya overy body shoki lol*}_


         *Washe Gari*
Da misalin 'karfe tara na safiya me napep ya sauke nusaiba 'kofar gidan Ya Jabeer kamar yanda take kiran sunanshi, Hannunta d'auke da wani babban kwando da kuloli masu kyau a ciki, nocking tayi me gadi yace "waye 
Nusaiba tace nice "to ina zuwa da Sauri yanufi get d'in yabud'emata 'karamar 'kofa tashige.

A falo ta zauna tanata doka sallama, jabeer ne yafito jikinsa sanye da jallabiya milk colour me gajeren hannu "A Nusaiba kece da wannan safiyar, "nice yaya ina kwana
"Lafiya lao.
"Gashi Mama tace akawomaku, kai amma mungode.

"Yaya ina auntyn tamu mu gaisa sauri nake zankoma na tsaida me napep, tana ciki bari na gayama, yafad'a tare da nufar d'akin baccin nasu.

Kwance ya isketa idanunta bud'e ba bacci takeba, "kizo ga Nusaiba nan tazo Mama ta aikota zaku gaisa wucewa zatayi,

Wani yamutsa fuska tayi "haba tunda safe kuma, nikam ba yanzu zan fitaba kawai kacemata tabari mun gaisa wani lokacin idan tazo.
"Sabodame bazaku gaisa yanzuba tunda tazo, 
"Ni kawai fitarce yanzu banyi niyyaba kozan fitane saboda 'kanwarka.
"A'a amma kinsan ba dad'i mutum yazo har inda kake kuma ya bu'kaci ku gaisa kice a'a.

Cikin fushi tatashi zaune tare da d'agamashi Hannu "dakata Malam nifa banison abinda kakemin 'kanwatace dazakace dole saina fita mungaisa da ita da wannan safiyar, kaida take 'kanwarka kaje kun gaisa to kace nace ta gaida gida, banison yawan magana tana kaiwa nan a zancenta takoma ta kwanta.




Love u all my Fan's ๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹
[1/9, 9:14 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................22





Duk abinda suke fada kan kunne nusaiba saboda yanda Hussaina take d'aga murya, Haka jabeer yafito jiki a sanyaye cike da fara'a nusaiba ta kalleshi "Halan aunty tamu bata tashiba, idan tatashi a gaishemin da ita nizan wuce, 
"Wani busasshen murmushi jabeer yayi dan yasan Nusaibar tajiyosu kawai dai basarwa tayi, "to shikenan Ki gaida Mama ga wannan ki sallami me napep d'in ya mi'kamata d'ari biyar guda tasa Hannu biyu ta kar6a tare dayin godiya sannan tafice a gidan.


Da misalin 'karfe goma jabeer yafito cikin shiri, kafad'arsa rataye da jakar laptop, d'akin Husaina yanufa dan ganin kota tashi, wani babban abin takaici shine yanda yanda ya isketa kwance har yanzu kayan baccine jikinta, batada niyyar tashi.

'Karasawa yayi gab da ita sannan yad'an bubbuga gadon, juyowa tayi ta kalleshi "lafiya Malam,? Ta tambaya cike da rainin wayo.
"Lafiya lao na shirayane zan fita, yakamata ace kintashi ga break fast can Mama ta kawomamu kiyi serving d'ina sauri nake zan fita office muna ayyuka dayawa gashi harnayi latti yafad'a yana kallon had'addiyar agogon dake d'aure jikin hannunsa.

'Kara gyara kwanciyarta tayi tare da juyamai baya, "kaga Malam idan zakaje kayi break d'inka kawai kaje kayi dan naga Alamar yunwa kakeji ni ba yanzu zantashiba dan bansaba kalaci da wuriba.

"Yanzune da wuri kiduba kiga yanda rana ta fito...
"Kaga malam kaje kawai dan Allah banison hayaniya, tafad'a tare da jawo wayarta wacce takashe tun jiya ta kunna.
Message's ne suka ri'ka rige-rigen shigowa, wanda yawancinsu duk jiyan akayoamatasu sakamakon jin wayarta kulle.

Jabeer kuwa falo yakoma ya bud'e kulolin wacce d'aya take d'auke da wainar shinkafa sai miyar alayyahu, sannan gudar kular dake d'auke da farfesun hanta, sai plask shikuma d'auke da kunun gyad'a Wanda yaji tsan-tsar madara yayi fari kal.

Zubawa jabeer yayi a gaggauce yaci sannan yazuba kunun gyad'ar duk da son dayakemashi wanda yasha befi Rabin cup ba saboda saurin dayake.

Jakarsa ya d'auka sannan yafice, Har yanzu Hussaina na d'aki tanajin lokacin dame gadi yabudemar get yafice sannan itakuma tafito.

Kulolin data gani ajiye tashiga bud'ewa, take taji tsohuwar yunwar data tara ta tasomata da sauri takoma d'aki tasheka wanka, tazo gaban mirror ta murza lotion da powder sai man le6e tasama lallausan le6enta sannan tanufi wadrope ta d'auko kaya riga da siket na atamfa tasaka, fitowa tayi tazuba wainar tacika cikinta sannan tabi da lafiyayyaen kunun gyad'a Wanda dad'insa saida ya ratsata har tsakiyar kanta, tana gamawa tami'ke takoma kan three seater ta kishingid'a batare data kauda kayan dataci abincin ba.

Wayarta tajawo tafara karanta text messages farko massage d'in Hafiz tafara karo dashi, inda yake cewa.
_Haba babyna banyi tunanin akwai abinda zesa kirabu daniba, duk irin so da 'kaunar danike nunamaki kin d'aukesu 'karya kinje kin auri wani bayan kinriga kin dasamin bishiyar 'kaunarki a zuciyata, kin yaudareni Kin cuceni kuma kinci amanata, wama yasani ko inmutu saboda 'kaunarki, amma kisani idan har haka ta kasance Allah baze barkiba. Kihuta lafiya *Hafiz*_

 Tana gama karantawa wasu zafafan hawaye suka zubo a idanunta, tasa hannu ta goge, tana cewa "ina sonka Hafiz ina 'kaunarka banta6a jin son wani namijiba a duniya bayan kai, ko yanzu ina tare dakai bazan gujekaba komin rintsi.

Sunanshi ta lalubo sannan ta danna kira bugu d'aya ya d'auka nan tashiga bashi ha'kuri "dan Allah kayi ha'kuri Hafiz wallahi ba yaudararka nayiba, har yanzu sonka yana cikin zuciyata ba abinda ya canja, kaine kaja Hafiz da farko na d'auka karabani da budurcina saida naba wani namiji kaina sannan na tabbatar dabahaka bane, kaja na mallamakama wani namiji kaina bakaiba.

"Kada ki damu babyna ni inasonki haka kuma zan iya kasancewa dake akowane hali kike, kedai kawai kicigaba da 'kaunata kamar yanda nike 'kaunarki.

"Kada kadamu babu wani namiji a zuciyata sai kai, tafad'a tana goge hawayen dake fuskarta, to shikenan yimin murmushinnan naki me sanyayamin zuciya, wani 'kawataccen murmushi tasaki kamar Hafiz d'in yana gabanta, wani lafiyayyen kiss yasakarmata ta wayar Wanda yaratsa dukkan sassan jikinta, taji inama kawai taganta tare da Hafiz yanzu ya shayar da ita zumar 'kaunarsa.






Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ˜ณ
[1/11, 6:47 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................23




Da misalin 'karfe hud'u na yamma me napep ya sauke Zuby 'kofar gidan Hussaina, megadi tafara yima magana sannan ya bata izinin shigowa bayan yanemo hakan daga gurin matar gidan, da dallama zuby tashigo 'kawataccen falon, mutuwar tsaye tayi saboda yanda falon yayi amasifar burgeta, batayi tunanin zata tarar da 'kawarta cikin wannan daular ba tunda taga Auren ba cikin shiri akayishiba.

Hussaina ta katsemata tunaninta ta hanyar yimata "welcome my friend, tafad'a tare da kamo hannu Zuby ta xaunar da ita kan d'aya daga cikin luntsuma-luntsuman kujerun dake zagaye da makeken falon.

Bayan sun gaisa Hussaina ta gabatarma da zuby da ruwa da lemu, nan zuby ta zuba lemun tanasha amma duk hankalinta nakan yanda aka kashe dukiya aka 'kawatama Hussaina d'akinta, nan take wani 'kululun ba'kin ciki yazo ya tsayama Zuby a wuya, a zuciyarta tace "tabbas dole inyi yanda nayi na raba Hussaina da gidannan, idan bansamu Hafiz ya aureniba, zan dawoma jabeer, 'karama jabeer d'in ai dan yafi Hafiz kamun kai da kamala, nasan idan har nayi nasarar rabashi da Hussaina nikuma zanyi yanda nayi ya aureni inyi zamana cikin jindad'i da farinciki nima inhuta da l'ikema yayan masu kud'i  danikeyi, muddin idan nasamu nasarar auren jabeer zan mallakeshi kota halin 'ka'ka sannan dukiyarsa sai yanda nayi da ita nima lokacin zan faso gari 'ya'yan talakawa zasu ri'ka likemin kamar yanda a yanzu nake li'kema wasu........ 
Wani shu'umin murmushi tayi dan lokacin har hangota takeyi zaune a wannan babban falon a matsayin matar gidan tad'ora kafa d'aya kan d'aya ga yan'aiki durkushe gabanta tana bada owk.... _lol_


Zuby ta lula duniyar tunani Hussaina nata faman yimata magana amma ko Alama batajitaba, saida Hussainar ta ta6ota "lafiya 'kawata Tunanin me kikeyi... 

Saurin dawowa zuby tayi daga duniyar tunanin data Lula, "a'a ba kome kawai ina tunanin halin rayuwa, yau gidanmu tashi mukayi bamu d'ora tukunyaba ga babanmu bayada lafiya, tana kaiwa nan ta fashe da kuka. 

Wani irin tsananin tausayinta Yakama Hussaina dan tasan abinda Zuby tafad'a ba 'karya ko yanayin gidan dasuke zaune kad'ai ya Isa ka gane suna cikin Halin rayuwa. 
"Kada kudamu inshaAllah idan jabeer yadawo zansa ya taimaka maku.

Zuby ta'kara fashewa da wani kukan munafunci kamar da gaske "nagode 'kawata Allah saka da Alkhairi, "ba kome 'kawata kada kidamu ai munzama d'aya tafad'a tana bubbuga kafad'ar zuby alamar lallashi.

Suna cikin haka suka jiyo sallamar suduka suka maida hankalinsu ga 'kofar tare da amsa sallamar, Jabeer ne yashigo da sallama, ko kallon inda yake Hussaina batayiba saima kauda kanta datayi gefe tana danne-danne a wayarta.


: Da sauri Zuby ta sauka daga kan kujera ta dur'kusa har 'kasa ta gaida Jabeer da Fara'a ya amsa "Zuby ce yau a gidanmu kice kinzo gun mutuniyar taki kenan, "eh wlh munzo shan manshanun amarya tunda haka akayi Auren ba gayya sai dai kawai mukaji a sama, murmushi jabeer yayi yace "wlh kuwa kinsan Al'amarin ubangiji muma yanda abin yazomaku haka yazo mana, mudai fatanmu atayamu addu'a.
"To Allah sanya Alkhairinsa yakuma bada zamanan lafiya, "Ameen ya amsa sannan ya wuce bedroom.

Saida Zuby ta tabbatar da shigewarsa sannan ta kalli Hussaina "kawata amma yanaga kamar baki murna da dawowar angon naki naga ko irin tarbar nan ta sabbin ango da amarya bakiyimashiba.
Yamutsa fuska Hussaina tayi "ai wannan tarbar sai idan akwai soyayya tsakani akeyinta, nifa yanzu babu soyayyar jabeer ko d'igo a cikin zuciyata, dan wallahi daze sakeni danafi kowa farinciki.

Saida Zuby tad'an razana dajin maganar Hussaina a zuciyarta tace "nifa ta fad'i gasashshiya dan naga Alamar raba Wannan shashar da Jabeer abune mai sau'ki, amma a zahiri sai tadafa kafad'ar Hussaina cikin tsananin nuna damuwa tace "Amma Hussaina sabodame kike son rabuwa da jabeer, yanzu kina tunanin akwai macen dazata samu gwarzon namiji kamar jabeer tayi fatan rabuwa dashi? Amma bansaniba wai hausawa sunce duk wanda ta 'kone rumbunsa yasan inda toka ke tsada..... Bansaniba ko kinada wanda yafishine.

"Yauwa 'kawata anzo wajen, inada Wanda yafi jabeer nesa bakusaba, 
"Waye wannan? Zuby ta tambaya.
"hafiz mana, shine namijin da babu wani namijin daze maye gurbinsa a cikin zuciyata.

Wani sanyi Zuby taji ya ziyarci zuciyarta, dan tasan 'kawar tata zatayi ba one ba one, dan kuwa tasan Halin Hafiz sarai baze ta6a Auren Hussainaba, tunda hartayi aure kuma wani namiji ya jusanceta bashiba, dan itama abinda tahanshi aurenta kenan dan tariga tabashi kanta, shikuma tsarinshi baya auren macen da yasani a mace kafin aurensu, yasha fad'ama zubyn haka lokacin datake kwakwar ya aureta, to barantana kuma wacce wani namijin ya kusanta bashiba.

Kallonta zuby tayi, "wow 'kawata nafa manta da wannan guy d'in, gaskiya dole kike rud'ewa ki susuce akansa dan ya matu'kar iya soayayya, ga kuma iya........

Alamar tafiyar dasukaji yasa zuby yin shiru, jabeer ne yafito cikin shigar 'kanan kaya bakin wando da milk d'in riga sai 'kamshin turarensa ke tashi da Alama shigarsa wanka yayi, ganinshi yasa Zuby mi'kewa to 'kawata nizan wuce sai wani lokaci kuma.

Saurin tashi Hussaina tayi "d'an jirani mana, kallon jabeer tayi bako fara'a a fuskarta inason magana dakai, batajira amsarshiba tawuceshi zuwa bedroom, binta yayi daga baya, basufi minti goma da shigaba saiga Hussaina tadawo hannunta d'auke da bandir d'in yan d'ari biyar-biyar Sabbi fill tami'kama Zuby "kawata ga wannan akaima Baba, amsa Zuby tayi hannu na 'kyarma "nagode 'kawata nagode "kada kudamu 'kawata kunzama d'aya.

Nan tayimata sallama ta tafi tana mamakin sakarci irinna Hussaina ace kasamu miji wanda zaka juya haka amma har kana 'ko'karin rabuwa dashi.
Wani shu'umin murmushi tayi tare da cewa "Ni zuby zanyimaki Hankali Hussaina sai kingane ni  *Makira* ce (na Fiddausi sodangi) wataran sai kinzo gidannan namiki korar kare......







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป  shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ™†๐Ÿป
[1/12, 4:24 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page---------------------- 24




          *Bayan Sati biyu*
Hassana tana zaune gidan jabeer ne kawai amma babu wata kyautatawa irin ta ma'aurata dake shiga tsakaninta dashi daga 6angarenta.
A nashi 6angaren kuwa be tauyemata komeba, dan ba abinda tanema tarasa, abinci kuwa har jabeer yasaba da cin na restaurant dan ko sau d'aya Hussaina bata ta6ayin girki da sunan faranta ranshiba, kullum sai dai tadafa dai-dai cikinta tazauna taci idan tagama tatashi tabar plate nan, kullum haka zatabar gidan kace-kace hatta da gadon dasuke kwana batasan tagyaraba, duk da wannan abubuwan datakema jabeer amma bata Hanashi kanta idan yabu'kaci hakan, sauran abubuwanma tanayinsune wai kozeji haushi yasaketa amma ko kad'an beta6a nuna alamun ze rabu da itaba sai dai idan abin yademeshi ya zaunar da ita yari'ka mata nasiha, 

zata zauna ta saurareshi yana gamawa zatace "Allahu Akbar, kaga Malam idan wa'azi zakayi kaje masallaci akwai masu bu'katar haka dayawa bananba inda bazeyi wani tasiriba, nifa ba dole akayima akan saika zauna daniba idan bazaka iyaba ka sauwa'kemin, ni wallahi da saki a hannuna yake da tuni na sawwa'kema na huta, wannan wane irin nacine kamar ni kad'aice mace a duniya kasakeni ka auro wata mana.

Wani gajeren murmushi jabeer yayi mai cike da takaici, "Hussaina bazan sakekiba, kuma badan ina son kyautata makiba kuma badan bazan iya rabuwar dakeba, bako d'aya kawai bazan iya sakinkiba dan saboda darajar mahaifinki, amma kisani duk abubuwan dakikemin watarana sai kinyi nadama....

Dariya tayi "Hmm nadama badai inyi nadamar rabuwa dakaiba sai dai inyi farinciki, saboda ko yanzu karabu dani inada masoyin daze aureni yari'keni da daraja da 'kima fiye da ri'kon da kakemin...
Saukar wani lagfyayyen mari taji a kumatunta shine yahanata cigaba da magana tare da dafe kuncinta wanda yakemata tsananin rad'ad'i.
"Ka mareni... Wlh bazan yardaba, kuma wlh sai kayi nadamar wannan marin dakayimin azzalumi kawai.
Ganin yayo kanta yasa ta ruga da gudu tashige bedroom tare dasa key ta jingena da 'kofar tana maida numfashi.
Cike da takaici da ba'kinciki jabeer yabar gidan,

 **             **               **

Hassanace zaune tare da Momy da Daddy bayan sungama cin abincin rana, daddy yatashi ze fita kenan Momy tayi magana  "Alhj takira sunanshi, dakatawa yayi ya zuba mata idanu yana jiran jin abinda zatace, "nace wai yaushe Hassana zataje tagano gidan 'yar'uwarta yakamata ace kabarta taje yau kimanin sati biyu kenan dayin aurennan amma kahanani kahana yar'uwarta zuwa wannan wane irin abune, ta'karashe maganar cikin ladabi.

"Ba yanzuba, yafad'a tare da d'aure fuska, tun yaushe nake gayamaku lokacin zuwa gidan waccan yarinayar beyiba, idan lokaci yayi da kaina zan umarci da aje, daga yau kada wanda ya'kara tunkarata da wannan maganar idanba so kuke ranku ya6aceba, yana gama fad'a yasa kai yafice.

Yana fita Hassana tafashe da kuka tare da fad'awa jikin Momy "yanzu Momy me hakan ke nufi, daddy yana nufin yarabani da 'yar'uwatane ko miye.

Kiyi ha'kuri hassana ba hakan yana nufin anrabaki da ita bane akwai dalilin dayasa Daddynku yahana muje amma ki 'kara ha'kuri inshaAllah bada dad'ewaba ze barki kije, haka Momy tayita rarrashin Hassana tana kwantar mata da Hankali.

**              **                 **

Da misalin 'karfe Hud'u na yamma Hussainace Zaune tanacin abinci jalouf d'in taliya tadafa da busashshen kifi, gefe kuma ga lemu tanaci tana korawa tana gamawa nan tabar sauran abincin tare da cup d'in datasha lemun, ringing d'in wayarta taji dake ma'kale jikin soket tana charge da sauri tatashi dan ta d'auko wayar tayi kwallo da kwalin lemun data rage Wanda ko rufeshi batayiba, nan yafad'i ya  zube kan carpet amma bata damuba saurin Isa tayi ta d'auko wayar ganin sunan Hafiz yasa tayi saurin danna OK tare da karawa a kunne.
"Hellow dear
"Haba babyna wannan wace irin rayuwace, Hafiz yafad'a cikin zafi-zafi.
Ace kullum muna tare a waya sai inkiraki yakai sau biyar arana amma kwata-kwata kin'ki kiyi dubarar dazamu had'u, gaskiya nalura kinfara son wannan mijin naki nike haukan banza, idan hakane kawai kifad'amin ni inha'kura.
Yayi 'kasa da murya kamar me shirin yin kuka "Amma idan kikamin haka kin yaudareni, tsakanina dake sai.... Be 'karasa maganarsaba ta tsinke wayar sakamakon jin Alamar shigowar mutum datayi, 

Nan jikinta yafara kyarma dan ance marar gaskiya ko cikin ruwa yayi ji6i, 

Sanye take cikin wani matsiyacin wando pencil, tare da wata d'amammiyar riga wacce ta sakko har gwiwa, kanta tayi rolling da wani shararan gyale Wanda behana ka hango gashin attach d'inda ke kanta, ga wasu muggan takalmi masu tsini dake 'kafarta. *Zuby kenan 'yar duniya Haya'kin taba*


Tsayawa tayi bakin 'kofar shigowa falon tana 'kara 'karema falon kallo, wani shu'umin murmushi tayi a zuciyarta tace "Allah kai damo ga harawa kobeciba yayi birgima, ma'ana idan nayi 'ko'karin raba jabeer da Hussaina koda be aureniba zanja ra'ayinshi ko zaman bariki muyi nikuma lokacin zan samu damar kwashe duk wani Abu daya mallaka in'kara gaba.







Love u all my Fan's ๐Ÿ‘ฏ. Oya sagem ๐Ÿ‘ฏ‍♂๐ŸŠ๐Ÿป‍♀
[1/13, 9:56 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................25

*Wannan shafin nakune masoyan wannan littafi*
*My Bestyn Nana, da kuma Ilham*
_nagode da kulawarku Allah bar zumunci_




"Welcome 'kawata ashe kece, Hussaina ta fafd'a tare da kamo hannunta ta Zaunar da ita kan kujera, Zuby tayi murmushi tace "wlh kuwa hanya ta biyo dani nace bara na le'ko mu gaisa, 
"amma kin kyauta kuma naji dad'in zuwanki domin dama ina Neman shawararki dan kobakizoba dama zan kiraki a waya.

To ai gani nazo 'kawata miye matsalarki? 
Shiru Hussaina tayi kafin ta numfasa, "Zuby kinsan dai irin son danikema Hafiz kuma nagayamaki muna waya dashi, to halin da'ake yanzu kullum idan mukayi waya sai yanunamin tsananin 6acin ransa akan na'ki yarda muhad'u, nikuma a gaskiya ina tsoron Daddy, kuma nasan jabeer baze barniba, kuma kinga nan gidan mijinane bekamata inkawoshi nan ba.

Murmushi zuby tayi a zuciyarta tace "Anzo wurin, da wannan damar zanyi amafani inraba Hussaina da jabeer, 
"haba 'kawata wannan aiba matsala bace zuby tafad'a tana kallon Hussaina.
"Husaaina tace kamar ya ba matsalaba kinsan fa akwai igiyar auren wani akaina kuma nike tarayya da wani namiji ina 'ko'karin had'uwa dashi kuma kice ba matsala bace.

Matsowa zuby tayi gab da Hussaina tare da kanga bakinta dai-dai kunnenta ta rad'amata wani magana. _(wanda koni zee bansan me tafad'a mataba)_

Suduka suka kyal-kyale da dariya tare da tafawa, Hussaina tace "Kai amma wannan shawarar tayi 'kawata shiyasa koda yaushe nake alfahari dake, kinga idan nayi haka zanje gurin masoyina inyi ko kwana nawa nakeso batare da wata matsala ba.

Nan take ta d'auko wayarta takira Hafiz bugu d'aya yad'aga tun kafin yayi magana tarigashi "hellow my dear ka shirya tarbar babbar ba'kuwa gobe-gobe.
"Kai haba da gaske? Hafiz ya tambaya cike da farin ciki.
"Da gaske mana kuma idan nazo kwana biyu zanyima.
"Wow babyna amma naji dad'i kice intashi inyima gidana general cleaning saboda zuwanki, 
Nan suka gama wayar zuby kuwa sai kallonta take tana wani shu'umin murmushi. 
Kafin ta mi'ke "to 'kawata nizan wuce kome kenan zamuyi waya, "to shikenan sai munyi wayar ko, har kusan get Hussaina tayima zuby rakiya, sannan tadawo.

Hussaina na dawowa ta d'auki wayarta takira Hassana 
"Hellow sister kina lafiya?
"Lafiya lao Husaina tafad'a, wai dan Allah sister yaushe zakizo gidana shikenan ace tunda aka kawoni keda Momy ba Wanda yazo.
"Hmm kedai bari sister wlh ko ranar nan saida mukayi maganar zuwana gidanki nida Momy wallahi bakiga fad'an da yayiba wai lokacin zuwa beyiba, idan lokacin yayi ze gayamin da kanshi.
"Hmm sister kema bakiyi niyyar zuwaba, kodayake nasanki da tsoro kamar farar kura, amma in bacin haka me zai hana idan kinfito islamiyya kitaho alabashi idan lokacin tashi yayi saiki koma.

"A'a sister nikam gaskiya bazan iyaba, kinsan halin dady muddin nayi haka yagane kinsan bazemin da sau'kiba,
"To shikenan sis yanzu nagane baki 'kaunata, amma danice ai duk yanda zanyi inzo gurinki zanyi tafad'a tare da fashewa da kuka.....
Hasaana Har cikin ranta taji tausayin 'yar'uwarta yakamata, "shikenan kibari zanyima Momy maganar idan ta amince inanan tafe goben, 
"To shikenan nasan ma Momy bazata'ki amincewaba, Allah kaimu goben ina jiranki.

Suna gama wayar jabeer nashigowa, tana ganin shigowarsa tayimashi wani mugun kallo up and down tare da buga wani uban tsaki "mtswww badai Zuciya, tafad'a tare da shigewa bedroom, kallo jabeer ya "karema falon yanda yayi kace-kace can plate nan cup nan robar ruwa, can ledar biscuit can kwalin lemu, ga kuma inda lemu ya zube ba'ayi mopping ba, girgiza kai kawai yayi sannan yanufi d'aki sai gashi yadawo sanye da best da wando threequter, plate da cups yafara kaudawa yakai kitchen sannan yad'auko mopper ya goge lemun daya zube, cikin 'kan'kanin lokaci yagyara falon fess, sannan yashiga kitchen yadafama kansihi indomie dan yadawo da yunwa, cikin minti goma ya gama ya zauna falo yaci.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘ฏ oya sagem ๐Ÿ‘ฏ‍♂๐Ÿ’ƒ๐Ÿป
[1/14, 8:13 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................26



*gaisuwa gareku masoyan wannan littafi*
*Mmn Ummi*
*mummy Ramadan*
*Mmn Zee*
*Mom Afreem*
*Allah rayamaku yaranku yayima rayuwarsu Albarka, Nagode Allah bar Zumunci*



Washe gari tunda 'karfe biyu na rana Hussaina ke faman bugama Hassana waya dan ta tabbatar da zatazo d'in kokuwa bazatazoba, 

Hassana na zaune kan kujera tana gyaran farce ta kalli Momy "Hmm kinga Hussaina ta isheni da waya A'kalla yau takirani yakai sau goma, wai dan Allah inzo gidanta kuma na gayamata daddy yahana yace lokaci beyiba amma ta nace da magiya, wai dan Allah in taimaka idan nafito islamiyya inje idan antaso sai indawo ai bazesan najeba shine nikuma nace gaskiya inajin tsoro amma bari in tambayeki idan kin amince sai inje.

Murmushi momy tayi "ba kome kije mana, amma kibari yanzu daddynku ze dawo, idan yadawo yaci abinci yafita, kekuma saiki shirya gurin 'karfe ukku saiki tafi, amma ki tabbatar da lokacin tashinku islamiyya yayi kidawo gida, "inshaAllah Momy aini kinsan banida matsala yanda nake tsoron Daddy inwuce mana ya 6allani cikin gidannan, murmushi Momy tayi "ah to nidai nagayamaki wlh.

Dai-dai lokacin kuwa daddy ya dawo Momy da Hassana sukayimashi sannu da zuwa, Momy ta kar6i jakar hannunshi suka wuce d'akinsa, bayan wani d'an lokqci suka fito tare daddy ya canja kaya da Alama wanka yayi, zama sukayi kan dining Hassana tayi serve d'insu bayan sun kammala cin abinci suka d'an ta6a fira, cikin firar tasune daddy ya kalli Hassana "watako kedai kin'ki fiddo miji kiyi aure ga 'yar'uwarki takusa wata d'aya a gidanta, 

Momy ce tace "Alhj to a ina zata samu mijin kullum tana 'kunshe a cikin gida, bata fita ko nan da can, yaushe wani ze ganta yace yanaso, indai ba itama irin na 'yar'uwarta zakamata ba.

"No no Hassana bazan ta6a yimata abinda nayima Hussainaba, saboda nutsuwarsuma ba d'ayaba, 
"To Allah dai yaza6a mata miji nagari, Momy tafad'a daddy ya amsa da "Ameen ya rabbi.
Sannan ya kalli Hassana "ki shirya yanzu idan zan fita in saukeki kigano 'yar'uwarki.

Wani irin tsalle tadaka cikin Farin ciki tanufi d'akinsu domin ta shirya.

 A gaggauce tafad'a toilet ta she'ka wanka tana fitowa tashafa ainafin cream d'inta coa-coa butter sannan ta murza farar powder, man le6e kawai tashafa sannan tanufi wadrope ta d'au'ko wasu kaya riga da zani d'inkin simple ta Sanya, dan tasan daddynsu baya 'kaunar 6ingilallun kaya da matsatsen siket koda ta sanya zesa taciresu.
Wani madai-daicin hijab ta saka sannan tafito nan sukayima Momy sallama suka wuce, momy har cikin ranta taji dad'in zuwan Hassana gidan Hussaina da Amincewar Alhjn, dan ita dama tun abinda Hussaina tayi take tsoron bada izinin zuwa wani guri batare da saninsaba, duk da tasan Halin Hassana yasha ban-ban dana Hussaina.

Dai-dai 'kofar gidan jabeer daddy ya sauke Hassana sannan ya ciro dubu d'aya yabata "ga wannan kihau napep 'karfe shidda tayimaki gida, "to daddy nagode Allah kiyaye hanya, 
Nocking d'in gidan tayi me gadi yataso yana tambayar waye tare da le'kowa ganin Hassana yasa yayi saurin bud'ewa tare da dur'kusawa ya gaisheta "Hajiya sannu da dawowa, wallahi banma kula da lokacin da kika fitaba, murmushi Hassana tayi dan tagane inda maganganun me gadin suka dosa a tunaninsa Hussainace, "Ba me gidan bace 'kanwartace tafad'a tana 'kara fad'ad'a fara'arta.
"To ikon Allah Amma kamarku tayi yawa gashi girmanku d'aya ba wanda ze iya ban-banceku, Allah me iko.....yafad'a yana ri'ke da baki.

Nan Hassana tawuceshi tabarshi cike da mamaki, yana wasi-wasi "Anya ba me gidan bace tafita, wata kila bataso asan tafita shiyasa tace ba itabace, amma in bacin haka ai kamar tayi yawa kome iri d'aya hatta da maganarsu ba ban-banci.
Wannan ai saiku rikita me gidan yakasa gane wacece tashi acikinku.
 ๐Ÿ˜‚


Zaune Hussaina take kan d'aya daga kujerun falon hannunta ri'ke da remote tana kallon wata wa'kar turanci a tashar music plus, wasu had'ad'un Riga da wando na Pakistan ne jikinta tasa gyalen kayan tayi rolling, ga 'kamshin wani had'adden turare dake tashi jikinta, kafarta sanye da takalmi plate me masifar kyau, gefe kuma 'yar'karamar jakartace wacce tazuba kayanta kala biyu a ciki, jiran zuwan Hassana kawai takeyi tatafi gurin Rabin ranta Hafiz dan tun d'azu yake kiranta a waya gani yake kamar bazatazoba.

Agogon wayarta ta duba 'karfe bud'u dai-dai gashi har yanzu Hassna batazoba wani guntun tsaki taja tare da lalubo sunanta ta danna kira sai jiyo ringing d'in wayar tayi a dai-dai kofar shigowa da sauri takai dubanta gurin ido hud'u sukayi da Hassana batasan lokacin data buga wani irin tsalleba cike da farin ciki ta makaleta "oyoyo my sister.



*Tofah Readers me Hussaina ke shirin aikatawane, Me take nufi da son zuwan Hassana gidanta, wace shawarace Zuby tabata duk kubiyo Zee Elkaseem (Mmn khady) yar mutan KATAINAWA domin samun cikakkiyar amsa a cikin littafin AUREN TAGWAYE*





Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป  shoki ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ‘Œ๐Ÿป
[1/15, 10:28 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................27



Cike da farinciki suduka suka fad'a kan kujera, Hussaina ta kalli Hassana wlh sister na d'auka bazakizoba harna fara cire rai, 

"Injiwaye inanan tafe ai,
 "amma naji dad'in zuwanki wlh, dariya Hassana tayi "lallai sister aurennan ya kar6eki kinga kuwa yanda kikayi kyau kikayi wani fresh, kamar kinje wata 'kasar Honey moon, dariya Hussaina tayi tare da kaimata duka cikin wasa "kai sister bakida dama, nidai yanzu bari nafara kawomaki lemu kisha idan kuma kina bu'katar abinci ga kitchen nan zaki iya shiga ki girka dan kema gidankine, bata jira jin abinda zata fad'ba tanufi kitchen tabud'e fridge domin d'aukoma sister dinta lemun.

Bayan shigarta kitchen kuma idon Hassana ya sauka kan jakar dake gefen Hussaina ajiye, hannu tasa ta d'auko jakar tare da zuge zip d'in ganin kayan sawa cikin jakar dakuma yan abubuwan bukata yabata mamaki, bata kai ga rufe jakar ba Hussaina ta dawo d'akin d'auke da lemu da cup d'in glass a hannunta ta ajiye gaban Hassana.

Kallonta Hassana tayi sannan ta tambayeta "sister wannan kayanfa na waye? Matsowa Hussaina tayi ta kar6i jakar ta rufe ta ajiye gefe sannan ta zubo lemun a cup ta mi'kamata "kar6i sister kisha zanyimaki bayanin kona miye....

Ba musu Hassana ta kar6i lemun ta shanye sannan ta kalli Hussaina "uhum ina jinki.

Cikin muryar Neman Alfarma Hussaina tafara magana "dan Allah sis wani taimako nakeso kiyimin wanda duk duniya nasan ba wanda zeyiminshi sai ke.
Cike da mamaki Hassana ke kallonta "ina sauraronki sister wane taimakone wannan?
 
Matsowa Hussaina ta'karayi kusa da ita "ba wani abu bane me wuya inaso ki zauna a gidannan a matsayina.....

"What? Hassana tafad'a tare da mi'kewa tsaye "me kike cewa sister ban fahimci inda zancenki ya dosaba, kama hannunta Hussaina tayi tare da maidata kan kujera ta zaunar da ita "plz sister ki saurareni mana nasan zaki fahimci inda zancena ya dosa.
"Ina jinki Hassana tafad'a tare da bin yar'uwar tata da kallo.

Hussaina tacigaba da magana "kamar yanda nafad'a inaso ki zauna a gidannan a matsayin nice, ba dad'ewa zakiyiba kwana biyu kawai zakiyi, kuma ni zaki taimaka.

"Kamar ya in taimakeki wannan abinda baze ta6a yiyuwa bane yaushe za'ace wani yayima wani zaman aure, aurefa ba abin wasa bane.

"Hmm sister dan Allah ki taimakamin inshaAllah ba abinda ze faru kuma ba Wanda ze gane, sanin kankine babu Wanda ke bam-banceni dake, ko Momy da daddy suna ban-bancemune ta gurin halayyarmu amma bata kamaninmuba.

"Dakata sister duk ba wannan ba, shin idan na zauna gidannan amatsayinki kekuma ina zaki?
"Yauwa sister tambayar dayakamata kiyimin kenan.
"Wata 'kawatace zatayi aure shine ta gayyaceni to na tambayi jabeer ya Hanani kuma yace idan nasake tunkararsa da maganar ze gayama daddy, to nikuma yanda nike da 'kawar tawa yawuce ace ta gayyaceni bikinta banjeba,

"To shine kuma baki iya zuwa rana d'aya ki dawo?
"Baze yiwu inje rana d'ayaba saboda ba nan garin bane.
"Wane garine? Hasana ta tambaya.
"Yar Kaduna ce, kuma kinsan nisan katsina zuwa Kaduna, kuma daga can Abuja zamu kai amarya kinga dole inkwana biyu.

Tana kaiwa nan a zancenta wayarta tashiga ringing tana dubawa taga sunan Hafiz gabanta yayi mummunan fad'uwa da kamar bazata d'agaba ganin Hassana ta tsareta da ido yasa ta d'aga "Heelow dan Allah kiyi Ha'kuri bani nacemiki zanzoba to yanzu haka wayar damuke ina hanya. Bata jira me Hafiz ze fad'aba ta tsinke wayar. 
"Kinganiko sister wallahi tund'azu takemin waya, Amaryar cefa.

Hassana cikin sanyin jiki tace "shikenan na amince zan Zauna amatsayinki "Amma ba nan gizo ke sa'kar ba ya zamuyi da daddy da Momy kinsan  dole zasu nemeni......

Saurin katseta Hussaina tayi tare da dafa kafad'arta "indan wannan kada kidamu, ni zantafi da wayarki zan barmiki tawa koda su daddy sunkira nasan bayanin dazanyimasu.

"To shikenan Hassana tafad'a, kawai dai ta amince da bu'katar 'yar'uwar tata badan komeba sai dan taga yanda ta masifar shiga damuwa, amma can 'kar'kashin zuciyarta cike take da tsoro da fargabar abinda suke shirin aikatawa.

Nan Hussaina ta 'kar6i wayar Hassana ta kwafi Number Hafiz tasaka a wayar Hassana, wacce ke wayarta kuma tasata blacklist tare dayin delete d'in number daga wayarta sannan ta baiwa Hassana wayar.

Nan ta d'auki jakarta sukayi sallama da Hassana tatafi, tana fita takira Hafiz da number Hassana tafad'amashi tana hanya kuma idan ze kirata da wannan number ze kirata dan tabar waccan a gida.







Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป  shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀๐Ÿ˜
[1/17, 9:19 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................28



Gabanta yashiga dukan tara-tara a zuciyarta tarin'ka tunanin taya zatayi zaman aure da mijin 'yar'uwarta, bayan ba mutuwa tayiba, kuma ba rabuwa sukayba, lallai Hussaina tasakata matsala sai yanzu takejin dama bata amince da 'kudirintaba, amma yanzu aikin gama ya gama dole ta zauna tarufama 'yar'uwarta asiri har lokacin dazata dawo, da wannan tunanin taji ana kiraye-kurayen sallar magrib saboda haka da sauri tanufi bedroom tashiga toilet ta d'auro Al'wala ta kabbara sallah, bayan ta idar da sallar ta dawo falo tsayawa tayi tana tunanin yanda zata fara aiwatar da ayyukan gidan dan da Alama Hussaina duk yau bata gyara gidanba, 

Sharar falon tafarayi, tare da yin mopping, sannan tasaka wani 'karamin towel me haske ta goge TV, center table, dakuma dining da sauran guraren da yakamata a goge, bayan ta kammala nan takoma bedroom, ta gayara tashare tare da canjama gadon bedsheet, lokaci guda gidan yayi fes kamar bashiba, freshner ta d'auko me dad'in 'kamshi ta feshe ko'ina hatta da toilet saida tagayara ta fesa freshener abin gwanin sha'awa gidan sai yakoma kamar wani Sabin kaya aka zuba saboda tunda yake Hussaina bata ta6a gyarashiba, kullum saidai ta 6ata.

Bayan ta kammala wannan kitchen tanufa nanma tsayawa tayi tana tunanin me zata dafa, dan tasan duk inda me gidan yake yana gab da dawowa duk da batasan lokacin dawowar tasaba, ta dad'e haka daga 'karshe ta yanke shawarar dafa abu mai sau'ki dan dare yafara gashi anata kiraye-kirayen sallar isha'i.

Jalouf d'in kus-kus ta dafa wanda yaji kayan lambu da kayan 'kamshi, sannan tayi amfani da tsoka nama zallah ta yankata 'kanana aciki yanda ze zamana duk lokacin da wanda zeci ya ebo yakai baki ze had'o da naman, dayake kus-kus ne cikin minti ashirin ta kammala dahuwar ta juye a flask, tare da had'a zo6o had'add'e shima sai 'kamahin flavour yake ta jera kan dining.

Bedroom takoma tafad'a toilet ta she'ka wanka, bayan tafito bata wani 6ata lokaci gurin yin kwalliyaba lotion kawai ta murza tare da 'yar hoda sai man le6e, wadrope tanufa ta d'auko wani had'adden less d'inkin Riga da siket ta sanya, wow kayan kuwa sun masifar kar6ar jikinta kamar dama dan ita aka d'inkasu, duk wata sura ta jikinta ta bayyana.

Zama tayi falo tare da jawo wayar da Husaina ta barmata tashiga danne-danne, tana dubawa tashiga inbox bataga komeba, sannan tashiga chat nanma ba kome, dan Hussaina batabar komeba saida tayi delete, dan kada Hassana taga halin datake ciki.

**                 **                **


Daddy ne ke safa da marwa hannunshi ri'ke da waya yanata try number Hassana amma sai acemai switch off, abin na matukar bashi mamaki gashi kuma har 'karfe tara na 'ko'karinyi bata dawo gidaba, Momy kuwa hankalinta yayi 'kololuwar tashi "innalillahi Alhj yanzu ina yarinyar nan tashige, anya kuwa lafiya dan bata ta6a yimana hakaba,

Juyowa daddy yayi ya kalleta shima Hankalinsa a tashe, yace "ni kaina ina mamakin hakan dan Hassana yarinyace me matu'kar tsoro da kiyaye fushinmu amma yau ace tawuce ka'idar dana gindaya mata, 

Momy wacce idanunta suka fara kawo kwallah tace bari inkira number Hussaina inji idan Hassana ta taho,  wayarta ta d'auko ta lalubo sunan Hussaina tanata ringing ba'a d'agaba dan ganin sunan Momy a wayar ba 'karamin d'aga hankalin Hassana tayiba, dan tasan duk yanda akayi yanzu itada Daddy sunacan hankalinsu yatashi na rashin dawowarta gida,  bata d'aga wayarba saida kiran Momy na hud'u yashigo sannan ta d'auka ta dannan OK tare da karawa a kunnenta saida ta dai-daita nutsuwarta sannan tace "Assalamu Alaikum.
A d'ayan 6angaren Momy cikin 6acin rai tace Hussaina kina ina inata kiran wayarki har kusan sau hud'u baki d'agaba.

Ba 'karamin fad'uwar gaba Hassana tayiba, tare da daburcewa dan gani take kamar Momy zata iya ganeta.
"Uhn ah am.... Dama bani kusa da wayar ne sai yanzu naji.
"To dama tambayarki zamuyi shin Hassana ta taho gida kuwa.?
"Eh tataho momy ai tun d'azu ta taho tace daddy yace kada ta wuce 'karfe shidda kuma biyar da rabi tabar gidannan.

"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Momy tafad'a tare da fashewa da kuka, tama manta ko tsinke kiran batayiba, Hassana kuwa tsayawa tayi ri'ke da waya a kunnenta tana sauraren yanda Momy ke kuka tana gayama daddy cewa "tun 'karfe biyar da rabi Hassana tabaro gidan Hussaina.
"Subhannallah Daddy yafad'a tare da cewa Allah bayyana mamu ita a duk inda take. 

Tsinke kiran Hassana tayi tare da sake kiran Momy, ringing d'aya ta d'auka, Nan Hassana ke tambayar "Momy wai meke faruwane, naji kinkira kintambayeni nabaki amsa kuma kinsa salati.
"Hussaina 'yar'uwarki Hassana har yanzu bata dawo gidaba kuma munkira wayarta switch off, 

"Innalillahiwa'inna'ilaijirraji'un Hassana tafad'a tare da fashewa da kuka, kafin ta tsinke kiran.
A tunanin momy Hassana tana kukane saboda 6atan 'yar'uwarta.
Itako Hassana kukan nadama da ba'kin cikin halin dasuka jefa iyayensu takeyi, sai yanzu take datasanin yarda da kud'irin 'yar'uwarta.





Love u all my Fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐ŸŠ๐Ÿป‍♀. ๐Ÿค’
[1/22, 6:47 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................29



Zaune take kan d'aya daga cikin kujerun dake zagaye da falon ta buga uban tagumi hannu bibbiyu, ba abinda take tunani sai halin da iyayenta suke ciki,

A zahiri tayi magana "nidai bari inkira Hussaina tadawo gidanta nikuma inkoma gida in fuskanci kowane irin hukunci daddy zeyimin koda kuwa zefi na Hussainar tsanani, dan bazan iya zama cikin tunani da fargaba ba.
Wayarta ta jawo talulobo sunanta ta danna kira amma kuma cikin rashin sa'a sai akacemata wayar akashe, "ya salam tafad'a tare da d'ora hannu bisa kai nashiga ukku, tafad'a tare da mi'kewa tsaye  "kodai inyi tafiyata idan tadawo tamasu bayanin inda taje, "kai bazan iyayima sister hakaba, muddin nasan daddy yaji labarin tayi wannan tafiyar kasheta kad'ai ne bazeyiba....
Wayyo ni Hassana ansakani tsaka me yuwa tafad'a tare da komawa ta zauna kan kujera jiki duk ba lakka.

Horn d'in mota taji gabantane yayi wani mummunan fad'uwa da sauri tanufi window tad'ga labulen tare le'kawa, me gadi ta hango yana 'ko'karin bud'e get, bayan ya bud'e motar jabeer tashigo duk kan idon Hassana yayi parking sannan yafito hannunsa d'auke da jakarsa, da sauri takoma ta zauna sannan tayi 'ko'karin dai-daita nutsuwarta dukda mummunan fad'uwar gaban datakeyi.

Da sallama yashigo falon, Hassana na Zaune jikinta sai kyarma yake tana tunanin wace irin tarba zatayima mijin 'yar'uwar tata, da kyar tasamu ta dai-daita nutsuwarta tare da mi'kewa ta dur'kusa ta kar6i jakar hannunshi tana mashi sannu da Zuwa, jabeer kuwa tsananin mamakine ya lullu6eshi yayi tsaye inda yake yakasa motsawa yayinda itakuma Hassana ta dad'e da shigewa d'akinsa domin ajiyemar jakarsa.

Murmushi yayi a Zuciyarshi kuma yace "ikon Allah, yau kuma ni Hussaina kema wannan tarbar, bin ko'ina na falon yayi da kallo ya ganshi fes-fea ba kamar yanda yasaba ganinshiba kullum kace-kace, sannan tunda yashigo daddad'an 'kamshin girki dana freshner sun had'u sun dakar mai hanci, lumshe idonshi yayi tare dayin wani guntun murmushi sannan yanufi d'akin dai-dai Hassana itakuma zata fito daga d'akin kad'an yarage suyi karo da juna Hassanar tayi saurin ja da baya duk tawani daburce "um ga ruwan wanka can nahad'ama "To, kawai jabeer ya iya amsawa dashi tare da binta da kallon mamaki sannan ya wuce Zuwa toilet d'in, tana ganin shigarsa tayi saurin zuwa wadrope ta fiddo mashi 'kananan kaya marar nauyi tare da ajiyesu gefen gado sannan tafita zuwa falo.


: Yana fitowa daga wankan yayi tozali da kayan da Hassana ta ajiyemai murmushi yayi saida ya murza mai sannan ya d'auki kayan ya sanya tare da feshe jikinsa da daddad'an turarensa, sannan yafito zuwa falo, zaune take kan kujera da waya hannunta tund'azu number Husaaina kawai take try amma switch off, dan tunda jabeer yadawo hankalinta yayi matu'kar tashi jikinta keta kar-karwa tsoronta d'aya kada jabeer yagane ita ba matarshi bace.


Da sauri ta tashi tana mashi sannu da fitowa, tanufi dining ta zauna sannan ta kalleshi "bissmillah mana tafad'a tare da gyaramashi kujerar daze zauna, ba musu yazo ya zauna yana binta da kallon mamaki danshi har yanzu abubuwan dake faruwa ganinsu yake kamar a mafarki wai yau shine Hussaina ke tarairaya haka lallai da walaki amma koma miye ba yanzu yakamata in tambayetaba.

Yana cikin wannan tunanin harta zubamar abincin ta ajiye gabanshi sannan itama ta zuba nata, haka suka faraci dad'in abincin na ratsa jabeer har tsakiyar kanshi, a zuciyarshi yana cewa "yaushe rabon dayaci abinci me dad'in haka kullum yana hanyar zuwa restaurant,  

Da misalin 'karfe tara da rabi na dare suna zaune falo kowanensu yayi ahiru wani Indian film suke kallo a tashar zee cinema, da Alama film d'in yayima Hassana kyau dan ta maida hankalinta kaf kan film din, yayinda jabeer bacci yacikamar ido, sai hamma yake d'aya bayan d'aya tasowa yayi daga kujerer dayake  yazo inda Hussaina take zaune Yakama hannunta "Taso muje mu kwanta, wani mummunan fad'uwar gaba taji tayi saurin kwace hannunta Daga nashi tace kaje ina zuwa saina ida kallon wannan film d'in.

Juyawa yayi ya kalli TV cike da mamaki dan yasan Hussaina bata ta6a yimar musuba idan ya umarceta dasu kwanta, kuma da kallo be dametaba, da wannan tunanin ya wuce d'aki yayi kwanciyarsa kasancewar akwai gajiya jikinsa bacci yayi gaggawar d'aukarsa.








Love u all my Fan's ๐Ÿ’ž๐Ÿ’˜๐Ÿ’ž๐Ÿ’•๐Ÿ’–๐Ÿ˜˜
[1/26, 10:09 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................30



Husaaina kuwa bayan ta isa gidan Hafiz, cike da murna da jin dad'in zuwanta ya tarbeta, tana isa takira Zuby a waya, ringing d'aya zubyn ta d'auka dama jiran kiran takeyi.

"Hellow 'kawata Zuby tafad'a cike da 'kagara taji abinda Husaainar zata fad'a mata.
"Kawata naji dad'in shawarar da kikabani dan yanzu haka ina tare da mutumin, 
Dariya zuby tayi a ranta tace "Zaki gane kurenki zaki gane da zuby kike magana.
Amma a zahiri sai tace "ai dama nagayamaki hakan kawai zakiyi kije inda ranki keso kiyi ko kwana nawa kikeso batare da wata matsala ba.
"Ai shiyasa nake masifar sonki 'kawata Hussaina tafad'a.
Zuby tace "ai nima banida kamarki shiyasa kullum nakeson ki kasance cikin farin ciki, da haka sukayi sallama, kowace ta ajiye wayar

Wata mahaukaciyar dariya zuby tayi tare da tafa hannu " yarinya kinshiga tarkona kad'an yarage in cimma manufata akanki,
Wata sabuwar dariya ta'kara kafin tasha mur kamar bata ta6a dariyaba "Hussaina ina me tabbatar maki yanda kika baro gidan jabeer kin barshi kenan Har abada.

Hussaina kuwa bayan sun gama waya da zuby toilet tashiga ta she'ka wanka, bayan tafito tabi jikinta da lafiyayyen lotion dinta tashafa kayan jikinta ta maida sannan tadawo falo ta zauna tana jiran shigowar Hafiz dan bayan sallar isha'i yafita yo masu take a way.

Be dawo gidanba sai 'karfe tara da rabi lokacin Hussaina nadai zaune kan kujera a falo sai hamma take jerawa d'aya bayan d'aya, ga yunwa na addabarta ga kuma wani irin bacci dake fizgarta

Da sauri Hafiz ya isa gareta tare da ajiye ledar dake hannunsa gabanta, "sorry babyna na dad'e ko? Ya tambaya yana kallonta yanda take lumshe idanu da Alamar jin bacci tattare da ita.

"Uhm, kawai tace tare da 'Kara gyara zamanta kan kujerar datake, "sorry sorry babyna tafad'a tare da nufar kitchen, bayan yan mintoci ya fito hannunsa d'auke da plate da cukulla da cup's, gabanta yazo ya ajiye sannan yazuba masu abincin, da sauri Hussaina ta fara ci saida taji tayi dam sannan ta kora da lemu, toilet tanufa ta wanke bakinta tadawo kan kujerar datake tad'an kishingid'a cikin mintina biyar bacci yayi awon gaba da ita.


Hafiz Kuwa bayan shima ya kammala cin abincin tattara plate d'in yayi da cup's ya mayar kitchen sannan ya wuce bedroom yafad'a toilet yashe'ka wanka yana futowa ya shafa cream wasu tare da feshe jikinsa da turare, jikinsa sanye yake da vest da shortnicar falo yanufa har yanzu Hussaina na kwance inda yabarta kan kujera sai sharar baccinta takeyi,

Tsayawa yayi kanta saida yakaremata kallo, take wata matsananciyar Sha'awarta ta d'arsu a zuciyarsa ahankali yakai hannunsa jikinta yafara shafata yana mata irin salon dayasaba tayar mata da hankali.

Can cikin bacci taji ana ta6ata saurin bud'e ido tayi tare da saukesu kan Hafiz dake aikamata sakon wani shu'umin murmushi, ture hannunshi tayi daga jikinta "miye haka kake shirin aikatawa kasanfa da da yanzu ba d'aya bane, yanda nasaki jiki dakai a da nabaka duk abinda kakeso yanzu baze yuyuba.

Hafiz yad'an 6ata rai "Haba babyna sabodame zaki hanamin kanki?
"Saboda kwakwkwaran dalili, Hussaina tabashi amsa.
"Inaga babu wani dalili dazesa ki hanamin wannan lallausan jikin naki me tarin ni'ima, a da kika amince dani baranrantana kuma yanzu da kome zamuyi baza'a ganeba kawai ki amincemin mu shana, yafad'a tare da jawota jikinsa ya matseta gam.






*sai kunyi ha'kuri da typing saboda 'yar matsalar da wayana ya samu koda aka gyara sai naji duk ta canjamin typing d'inma baya sauri*





Love u all my fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐Ÿ‘„๐Ÿญ
[1/26, 3:05 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................31




®TALANTED WRITER'S GROUP (T.W.G) ๐Ÿ“



Saurin tureshi tayi daga jikinta tare da mi'kewa tsaye cikin 6acin rai take magana "haba Hafiz wannan wace irin rayuwace, kabar ganin nakawo kaina gareka hakan ba yana nufin zan mallaka maka duk abinda kake bu'kataba daga gareni, akwai dalilin dayasa na amince da zuwa gidanka harna baro gidan aurena, duk wannan maganganun Hussaina tanayinsune cikin tsananin fushi da matsananancin 6acin rai.

Ran hafiz ya 6aci da jin maganganun Hussaina  yayi niyyar gayamata magana kamar yanda gayamar amma sai wata zuciyar tace "fushi ba naka bane kabita a hankali har kasamu ha'karka ta cimma ruwa.

Cikin sanyin jiki hafiz ya dur'kusa gabanta shikenan babyna na ha'kura amma kitaso muje mu kwanta yafad'a tare da kama hannunta.

Fizge hannunta tayi daga rikon dayayimata tare da komawa kan kujera ta zauna tace "kaje kawai ni anan zan kwanta, tashi hafiz yayi yanufi bedroom jikinsa a sanyaye a zuciyarsa ba haka yasoba yaso ace ya kwashi gara ta hanyar kusantar Hussaina dan dama ya dad'e rabon dayayi mu'amula da wata mace tunda suka samu sa6ani da zuby kusan sati batazo gidanshiba wanda ada yasaba baya kwana biyu basu had'u suka she'ke ayarsuba.

Da haka ya haye gadonsa zuciyarsa fall da tunani "to miye amfanin zuwan wannan yarinyar guna tunda bazanji dad'i da itaba, amma bari inbarta inga iya gudun ruwanta zuwa gobe kuwa idan ta'ki amincewa zan danneta kota 'karfi, dan nariga na kwad'aitu da ni'imar jikinta da wannan tunanin bacci 6arawo yayi awon gaba dashi, yayinda Hussaina batayi wani baccin kirkiba sakamakon wani mummunan mafarki datayi da Hassana Hakan yasa ta yanke hukuncin komawa gida gobe dan ganin halin da 'yar'uwarta take ciki.

**                **                     **

 Kiraye-kirayen sallarY asubah yatashi jabeer daga bacci yakai hannunsa inda yake tunanin jin matarsa amma sai yaji wayam tunaninsa yakai ga tana toilet yadad'e yana jiran firowarta amma har ana niyyar kabbara sallah masallaci batafitoba ahankali ya tura 'kauren toilet d'in ganin bata ciki yabashi mamaki shiga yayi ya d'auro Alwala yafito falo ga mamakinsa ganinta yayi kwance kan kujera ta tada kanta da pilon kujerar tanata sharar bacci.


 Cike da mamaki jabeer ya'karema Hassana kallo wacce shi atunaninsa Hussainace a zuciyarsa yace "me hakan ke nufi Hussaina ta canja hali ta ko'ina tana kyautatamin amma kuma yanzu tana 'kauracema shimfid'ata sa6anin da da bata kyautata min amma kuma tana bani Ha'kkina na aure dan koban kirataba zata kawo kanta to kodai tana cikin lalurane, amma kotana lalurar fashin sallah tasan duk hanyar sazatabi ta biyamin bu'kata kuma bata ta6a 'kin kwana tare daniba, amma koma miye zan tambayeta inji dalili.

Da wannan tunanin yatasheta sannan ya umarceta dataje tayi sallah, ba musu tatashi cikinagagin bacci tanufi toilet ta d'auro Alwala ta kabbara sallah, shikuma ya wuce massallaci dan gabatar da tashi sallar.

 Bayan an idar da sallah jabeer yadawo gida tundaga falo yake jiyo sautin karatun al'qur'anin da Hassana ke rerawa abin ya matu'kar bashi mamaki dan yasan tunda yake da Hussaina bata ta6a yin karatun Qur'anic irin wannan lokacinba,  cike da mamaki ya wuce bedroom yahaye gado ya kwanta yana sauraren yanda karatun ke ratsa kwalwarsa cikin zazza'kar muryarta.

Saida tayi da yawa sannan ta tsaya tayi addu'a tashafa inda jabeer yake kwance taje  ta zauna nesa dashi cikin ladabi tace "barka da kwana 
"Barka dai jabeer yafad'a batare daya d'ago daga kwancen dayakeba.
"Antashi lafiya? Takuma tambayarsa "lafiya lao, ya amsa tare da gyara kwanciyarsa.

Daga nan bata 'kara maganaba tafito tanufi kitchen domin sama masu abin karyawa.







Love u all my fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐Ÿ‘„๐Ÿฌ
[1/28, 8:12 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page...................... 32



®TALENTED WRITER'S GROUP (TWG) ๐Ÿ“


Gidansu Hassana kuwa Hankalinsu yayi matu'kar tashi ganin ankwana d'aya ba Hassana ba labarinta, Momy tayi kuka harta godema Allah yayinda dady yarasa sukuni ankai report police station sannan daddy da kanasa yaje duk wani babban asibiti dake garin ko Allah zesa yaga Hassana koda kuwa gawartane hankalinsu ya kwanta anma kome kama da ita be ganiba.

Dole ya hakura ya dawo gida ya zauna hankali a tashe yasaka cigiya gidajen redio da television,

Maganar 6atan Hassana ta bud'e ko'ina 'yan'uwa da abokan arzi'ki sai zuwa suke jaje, Momy Kuwa kuka kawai take idanunta sun kumbura abinci kuwa sai dai tad'an tuttura abinda ya sauwa'ka dan abincinma d'acinsa takeji ga matsanancin ciwon kai dake addabarta.

**                **                  **


Da misalin 'karfe takwas ta kammala had'a masu breakfast ta jera kome a dining Sannan ta hau gyaran d'akin duk da bawani datti yayiba ta 'kara gyarashi ta share sannan ta kunna turaren wuta, a hankali ta tura 'kofar bedroom d'in wani dad'i taji ganin jabeer baya d'akin saboda haka da sauri tashige tare da maida 'kofar ra rufe hada sa key. A gaggauce ta gyara d'akin ta goge ko'ina sannan ta feshe da freshener, kayan jikinta ta cire ta d'aura wani 'karamin towel tafad'a toilet ta she'ka wanka bayan tafito gaban dressing mirror ta tsaya simple makeup' tayi sannan tanufi wadrope wasu riga da siket na less tasaka, kayan sun masifar fito da ainafin kyawunta dukda ba wata kwalliya tayiba.

Lokacin kuma jabeer yafito cikin shirinsa sanye yake cikin 'kananun kaya milk d'in riga da ba'kin wando 'kafarsa sanye da ba'kin takalmi yan kamfanin masaraci, hannunsa ri'ke da jakarsa ta Zuwa office, ajiye jakar yayi kan kujera sannan yanufi d'akin da Hassana take tura 'kyauren d'akin yayi da mamakinsa sai yajishi gar'kame da key, saboda haka nocking yayi sannan yanufi dining ya zauna yana jiran fitowarta dan bayaso ya makara office dan yanzu ayyuka duk sun dawo  hannunsa saboda daddy baya fita office saboda 6atan Hassana


Saida gabanta yayi 'yar'karamar fad'uwa lokacin da jabeer yata6a kyauren d'akin.

Jiki a sanyaye ta bud'e tafito kan dining ta hangeshi saboda haka can tanufa tana takunta cikin nutsuwa, idanuwa jabeer ya 'kuramata ko 'kiftawa beyi wata matsananciyar sha'awarta ke fizgarshi dan jabeer irin mutanannane masu 'karfin sha'awa dan baze iya kwana biyu batare daya kusanci matarshiba kuma itama ta sabamai da hakan dan kobe nemetaba take kai kanta gareshi shikuma bewuce tayi. _lol_

Jitayi dukta tsargu da kallon dayake mata, ba 'karamar dauriya tayiba lokacin data iso taja kujera d'aya ta zauna sannan ta fara zubamar kalacin duk illahirin jikinta kyarma yake.

Haka suka fara breakfast d'in bayan sun kammala ne jabeer ya kalli Hassana yace "waini Hussaina kwana biyu naga kin canjamin kinayimin duk wani Abu dakikasan ze faranta raina sa6anin da davaki damu da damuwataba.

Murmushi tayi "kada ka damu mijina kasan Allah ba yanda baya sauya Al'amarinsa jiya ina zaune ina kallon TV aka sanyo wani malami yana wa'azi, to wa'azin dana tsaya na saurara sainaji kamar hallayatace kaf yake zayyanawa sannan kuma tafad'i irin azabar da Allah yatanada ga mata masu irin halayyarmu shine nikuma abin yad'agamin hankali.

Cike dajin dad'i jabeer yace "kai amma Allah yayima wannan malamin Al'barka 
Hassana ta amsa da "Ameen.

Shiru yad'an ratsa nayan mintittika kafin jabeer ya'kara magana karo na biyu "to amma malamin beyi magana kan matar dake "kauracewa shimfid'ar mijintaba dakuma irin azabobin da Allah ya tanadar mata.






Love u all my fan's ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป shoki ๐Ÿ‘„๐Ÿฆ
[1/30, 9:01 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................33




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Shiru Hussaina tayi dan batada cikakkiyar Amsar dazatabashi akan wannan tambayar da yayimata, ganin batada niyyar magana yasashi mi'kewa tare da d'aukar jakarsa "ni zan wuce wurin aiki "Allah kiyaye hanya kawai tacemasa batare data motsa daga inda takeba.

Yana fita ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya da sauri tanufi bedroom waya ta d'auko ta shiga laluben sunan Hussaina sannan ta danna kira cikin sa'a kuwa tasamu wayar na ringing amma harta tsinke ba'a d'agaba, batayi 'kasa a gwiwaba ta'kara kira karo na biyu nanma tanata ringing sai gab da zata tsinke sannan aka d'aga 
"Hussainace tafara magana Hellow sister ai ganinan ina shiri inshaAllah yau zandawo yanzuma bada dad'ewaba.

Wata ajiyar zuciya Hassana tayi "nidai dan Allah ki dawo kinga muna shiga hakkin mijinki saboda na kula irin mutanennane mabu'kata nikuma kinga ba yanda za'ayi inbiyamasa dan Allah ki dawo saboda gudunmatsala.

Kada ki damu sister inshaAllah yau zandawo "To shikenan tafad'a tare da ajiye wayar kan mirror datake kwalliya gabanshi, 
gefe kuma ga jakar kayanta da sauri tagama kwalliya sannan ta jawo jakar taciro wani riga da zani na atamfa ta sanya sannan ta d'aura d'ankwalin kayan wata madaidaiciyar hijab tasaka sannan takoma bakin gado tazauna tana jiran dawowar Hafiz, tund'azu yafita be dawoba shi kawai take jira gashi har 'karfe sha d'aya da mintittika, 'kara duba agogon wayarta tayi lokaci naja wani d'an guntun tsaki tayi tare da ajiye wayar gefenta ta sadda kanta 'kasa tunanin yanda zasuyi Hassana takoma gida batare da wata matsalaba takeyi dan tafi kowa sanin halin daddy.

Wata zuciyar tace ki kira zuby tunda itace tabaki wannan shawara itakad'ai kuma zata baki shawarar yanda za'ayi Hassana takoma gida batare da ansamu wata matsalaba.

Murmushi tayi tare da mi'kewa dan d'auko wayarta, gabantane yayi wani mummunan fad'uwa lokacin dasukayi ido hud'u da ita, sanye take cikin wani matsatstsen wando da wata figigiyar riga wacce da kad'an tawuce 'kugunta  sai wani yabud'ad'd'en gyale datayi rolling dashi fuskarta ba Alamar fara'a ko kad'an.

Cike da mamaki Huasaina ta kalleta tare da fad'uwar gaba, dakewa tayi ta tanufo inda take tsaye ta maida hannuwanta baya tanayima Hussaina wani shu'umin kallo.

"Naji dad'in zuwanki 'kawata kamar kinsan dama yanzu nake 'ko'karin kiranki, Hussaina tafad'a tana fad'ad'a murmushin dake fuskarta.


 'Kara d'addaurewa Zuby tayi ba Alamar wasa tattare da ita, duk da haka Hussaina daurewa tayi tacigaba da kusanto inda zuby take, batayi auneba sai jitayi zuby ta hankad'ata iya 'karfinta tayi taga-taga zata fad'i da kyar tasamu ta daddafe ta kalli zuby wacce ke 'kara tinkarota har yanzu dai hannunta d'aya na bayanata, 'kara Hankad'a Hussaina tayi iya 'karfinta wannan karon saida tayi nasarar kayar da ita.

Wata irin fad'uwa Husaainar tayi kanta ya bugu da gefen gado take gurin yafashe yafara zubar jini, Hannu Hussaina tasa ta dafe gurin tana kallon zuby dake tunkarota Hannunta ri'ke da wani 'katon icce.

Cike da tsoro da fargba Hussaina ke 'ko'karin mi'kewa dan samun matsera dan taga Alamar ba wasa ko kad'an a idon zuby kuma ba Alamar d'igon imani tare da ita.

Ganin Hussaina na 'ko'karin mi'kewa yasa Zuby d'aga iccen dake hannunta ta kwantarama Hussaina akai, nan take ta zube jini yagama wankemata fuska, ta kalli Zuby cikin 'karfin hali da kyar ta iya d'aga bakinta tayimata magana.

"Zuby me nayimaki kike neman kasheni, mena tsaremaki a rayuwa?

Wata mahaukaciyar dariya zuby ta gagga6e da ita sannan ta d'addaure kamar bata ta6a dariyaba, sannan ta du'ko dai-dai inda Hussaina take kwance male-male cikin jini tana maida numfashi da kyar tace "Kin taremin kome a duniya Hussaina na dad'e ina ba'kincikin kasancewarki d'iyar masu kud'i nikuma d'iyar talakawa wad'anda talauci yayima kanta.

Sannan na dad'e ina mutuwar son Hafiz beta6a nunamin soyayyaba dai-dai da rana d'aya sai dai yana biyan bu'katarshi dani aduk lokacin daya bu'kaci hakan.
Amma lokaci guda ya nuna ba wacce yakeso sai ke, tafad'a tana nunata da yatsa.

Sannan tami'ke tsaye tayi taku biyu zuwa ukku "ban 'kara shiga tashin hankaliba sai ranar danaje gidanki mijinki yayimin kyautar kudad'e masu yawa tundaga lokacin naji ba wanda nakeso samada mijinki jabeer kuma naci Al'washin sai yazama mallakina.

Na zauna nayi tunani nayi nazari naga ba yanda za'ayi insamu biyan bu'kata saita hanyar kawar dake daga doron duniya.

Hussaina najin haka wani irin kuka da nadama sukazomata lokaci guda.

Zuby kuwa ba tausayi ba imani tacigaba da bugun Hussaina aka da wannan 'katon iccen saida ta tabbatar da babu sauran numfashi tattare da ita sannan tayi saurin barin gidan.







Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„
[1/31, 9:13 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................34




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“


*Gaisuwa gareku masoyan wannan littafi wannan shafin nakune Mummy Ramadan da Bilkisu Mu'azu (Bilma) Allah bar 'kauna yakuma raya maku yaranku bisa tafarki na Addinin musulunci*


Da musalin 'karfe biyar na yamma Hassanace Zaune itada jabeer sai janta yake da fira amma ita kwata-kwata hankalinta baya gurinsa itadai fatanta d'aya Hussaina tadawo itakuma ta koma gida dan yau ya kasance weekend jabeer be fita ko'inaba tun safe yake gida sai wani shu'umin kallo dayakebinta dashi.

Wayarta ta jawo tacigaba da try number Hussaina wacce tun misalin sha d'aya  na safe daaukayi waya ta gayamata tana hanya, tundaga lokacin kota kira sai tayi ringing tagama ba'a d'agaba, yanzu kuwa data kira cemata akayi (switch off) kashe take baki d'aya hankalinta ya'kara tashi ga jabeer yatasata gaba da Alama yanada bu'kata.


"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ta furta tana 'ko'karin 'kara try number Hussaina lokacin jabeer ya'karaso inda take zaune shima zama yayi kusa da ita har jikinsu na gugar na juna, Hannu yasa ya kar6e wayar tare da jawota yahad'ata da jikinsa "wai tund'azu wa kike faman kira haka kinbarni ni kad'ai sai fira nakemaki amma Sam hankalinki baya gurina yafad'a tare da ajiye wayar kan centre table, itakuwa Hassana yana Had'a jikinta da nashi jikinta yahau 6ari, kyarma take kamar mazari, shikuwa jabeer shiga yayi cikin wani irin yanayi me wuyar fassarawa, wata matsananciyar sha'awa ta'kara saukarmai lokacin yakai 'kololuwa gurin bu'katar mace.

Tureshi tafarayi tana 'ko'karin raba jikinta danashi, 
Lokacin ya fahimci halin datake ciki sakinta yayi tare da 'kuramata ido sannan ya kira sunanta cikin wata mabu'kaciyar murya "Hussaina 
"Na'am ta amsa batare data d'ago ta kalleshiba.
'Kara kiran sunanta yayi karo na biyu "Hussaina, d'agowa tayi ta kalleshi batare datakuma yin maganaba, gabanta yayi wani mummunan fad'uwa ganin irin cikin halinda jabeer yake ciki idanunsa sun kad'a sunyi ja, magana yafara muryarshi na sar'kewa kamar zeyi kuka "dan Allah ki taimakeni kibani ha'kkina sanin kankine ban iya neman matan banzaba kece halalina bekamata ki gujeniba, banida wanda ze d'aukemin wannan sai ke, kuma tun acan baya kinsabin da bani ha'kkina duk lokacin dana bu'kaci hakan amma cikin kwanaki biyu kingujeni, meyasa ? miye dalili? namaki wani laifine? ya'karashe maganar yana kallonta.


 Wani irin tausayinshi yakamata, batasan lokacin da wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanuntaba a zuciyarta tace "Hussaina kin cuci mijinki kinbarshi cikin wani hali wanda ni ban isa in fiddashiba,
Nikuma kinsani tsaka me yuwa, ya Allah ka kawomin d'auki.

Ganin hawaye a fuskarta yasa hankalin jabeer tashi yafara tambayarta "maganar danayimakice ta 6atamaki rai, indan wannanne kiyi ha'kuri nima na ha'kura, yana gama fad'in haka yatashi yanufi bedroom,

Minti sha biyar da shigarsa saigashi yafito sanye da wasu kayan ba Wanda yashiga dasuba ko kallon inda take beyiba yafice daga gidan, tanajin lokacin dame gadi yabud'emasa get yafice da motarsa, fad'awa tayi kan kujera tafashe da wani sabon kuka

Wayarta tajawo tasake kiran number Hussaina amsar dai d'ayace wayar na rufe baki d'aya.

Haka tacigaba da kukanta ita d'aya cikin gida bame rarrashinta, 

Da misalin 'karfe takwas na dare jabeer yadawo gidan hannunsa d'auke da leda da sallama yashigo falon, zaune take jikinta sanye da wata 'karamar hijab, sannu da zuwa tayimai tare da kar6ar ledar dake hannunsa fresh milk ce sai gasashshin kaji, zama sukayi tsakiyar kafet d'inda ke malale falon suka fara ci, jabeer ciyake sosai yayinda Hassana take d'an tutturawa dan batada wani sukunin cin abinci.

Duk abinda take yana kula da ita amma be tankamataba, saida yaci ya 'koshi sannan yabi da fresh milk itama madarar ta zuba ta kwankwad'a saitaji tamata dad'i saboda haka duka ta shanye tata, shikuwa jabeer daya gama dama d'aukar sauran nashi milk d'in yayi yanufi bedroom dinshi.







Love u all my Fan's ๐Ÿบ
[1/31, 9:20 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................35




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“


*Wannna shafin na masoyanane dake jihar River cikin birnin Fatakwal 'kar'kashin jagoranci Fadeelah Ammin yusrah nake mi'ka sa'kon gaisuwata gareku nagode daso da 'kaunar da kuka nunamin Allah 'kara dan'kon Zumunci*




Tana gama shan milk d'in taji kanta yamata nauyi duk illahirin jikinta yayi sanyi wani irin bacci ya rin'ka fizgarta duk abinda ke falon takoma ganinsa bibbiyu, da kyar tasamu ta isa bedroom tare dayin nasarar sa key ta kulle 'kofar sannan tafad'a gado ko sauya kayan jikinta batayiba zuwa na bacci.

Kusan minti goma da shigarta d'aki jabeer yafito daga gudan d'akin tura d'akin nata yayi amma sai yajishi gar'kame da key wani irin haushi ya 'kuleshi da sauri yakoma d'akinshi sai gashi yadawo da wani key d'in a hannunsa, sakashi yayi gurin key d'in 'kofar sannan ya murd'a 'Kofa kuwa ta bud'e shiga yayi d'akin haske fayau dan Hassana ko damar kashe fitilar d'akin bata samuba bacci me nauyi yayi awon gaba da ita.


Tsayawa yayi yakaremata kallo wata irin kwanciya datayi, wani Shu'min murmushi yayi sannan ya rage hasken d'akin ya maida 'kofar yarufe hayewa yayi kan gadon yajawota zuwa jikinsa yafara wasa da jikinta cikin 'kan-'kanin lokaci yabiya bu'katarsa da ita batare datasan inda kanta yakeba.

Saida ya gama abinda yake yafad'a tunani a Zuciyarsa yake cewa "yanaji Hussaina kamar budurwa wacce bata ta6a sanin namijiba abin da mamaki.

Wata zuciyar tacemai ba wani abu yasa kajita hakaba sai dan bada amimcewarta ka kusancetaba.
Nan take yayi na'am da abinda zuciyarsa ta raya masa sannan kuma ya tsinci kansa cikin tsananin farin ciki.

Ahaka bacci yayi awon gaba dashi yana rungume da hassana jiyake wani sabuwar 'kaunarta na'kara shigarsa

Kiran sallar asubar farko Hassana ta farka daga nannauyan baccin datayi, jinta jikin mutum yasata saurin ida bud'e idanunta dan tabbatarma kanta shin abinda taji da gaskene ko mafarki takeyi ganin jabeer kwance yana sharar bacci ga ya had'e jikinshi da nata ya wani rungumeta, ga jikinta ba kaya ko d'aya tana ganin haka tasan aikin gama ya gama, jabeer yagama biyan bu'katarsa da ita, wani 'kululun ba'kin ciki yazo ya tokareta batasan lokacin data fashe da wani irin kukaba.


 Kukanta yatashi jabeer daga nannauyan baccin dayakeyi me cike da Farin ciki, tambayarta yashigayi "lafiya Hussaina meyasaki kuka, a zuciyarta tace jabeer tsakanin kaida sister bansan wanda ya cuceniba sanadiyyar haka gashi narasa abinda kowace d'iya mace take ta'kama da tin'kaho dashi.

"Wayyo Allah nashiga ukku tafad'a hawaye nabin kumatunta wasu bayan wasu.
Jabeer kuwa 'kara jawota yayi jikinsa ya 'kara 'kan'kameta yana rarrashinta "please and please tell me, shiru tayimai dan batada amsar dazata bashi.
"Haba Hussaina ki gayamin abinda ke damunki duniya idan baki gayamin damuwarkiba amatsayina na mijinki waye zaki fad'amawa.

Hassana kuwa jitayi kamar tadad'amai tace "bafa matarka bace Hussaina ni 'yar'uwartace, saurin sa Hannu tayi ta toshe bakinta tana cigaba da kuka gani take kamar tunanunta zefito fili har jabeer yaji.

Ahankali ta zame daga jikinshi tana tafiya da kyar tanufi toilet tahad'a ruwan gumi tagasa jikinta sannan tayi wankan tsarki ta d'auro alwala tazo ta tada sallah lokacin shima jabeer yana d'akinsa wankan yayi tare da kabbara sallar a  zuciyarshi yana tunanin dalilin kukan matar tashi danya kusanceta Wanda ba yau suka faraba.

Bayan ta idar da sallah tana zaune kan abin sallar hawaye nacigaba da zuba daga idanunta jabeer yashigo d'akin zama yayi bakin gado yana fuskantarta ya kula da har yanzu kuka take ajiyar zuciya yayi sannan yace "Hussaina yau inaso ki gayamin dalilin 'kauracemin dakikayi kuma dan na kusanceki kike kuka kamar na kasheki.

A zuciyarta tace "kara kisa da abin kunyar dana aikata, nayi matu'kar danasani da amincewa da "kudirin 'yar'uwata.

Maganar jabeer ce tadawo da ita daga tunanin datake "zaki fad'amin kokuwa saina kira daddy 'kila shi ki fad'amasa.

Saurin d'agowa tayi da jajjayen idanunta ta kalli jabeer ba Alamar wasa tattare dashi, gabanta yayi mummunan fad'uwa kawai saita tsinci kanta da gayamashi "dama Hussaina ce...........






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿค”
[2/1, 11:19 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................36



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“


"Yanzu kamar ni ina matsayin mijinki ace ban isa ki gayamin damuwarkiba, to shikenan zan fad'ama Daddy 'kila shi kin gayamashi idan ya tambayeki amma kinsan bazan saka maki ido kina matsayin matataba inje waje innemi matan banza.

Bayan Hannu Hassana tasa ta share hawayen dake bin kumatunta sannan ta kalli jabeer cikin dasashshiyar murya take magana "Nifa ba wani abu bane ke damuna kawai ina tunanin 6atan "yar'uwatane yau kwana biyu ko labarinta ba'a samuba.

Tana kaiwa nan tafashe da wani sabon kuka, jabeer har cikin ranshi tabashi tausayi sosai janyota yayi jikinsa yana rarrashinta, da dabara tasamu ta kwace kanta tanufi kitchen domin had'a masu breakfast.

**                  **               **

Daddy zaune daga bakin gado kallo d'aya zakayimai ka tabbatar da tsananin damuwar dake tattare dashi, Momy kuma nakan abin sallah  tana lazimi idanunta fall da hawaye ro'kon Allah kawai take Allah bayyanar mata da d'iyarta aduk halin datake ciki,

Wayar daddy dake jone jikin socket tana chaji tahau ruri alamar shigowar kira, ko motsawa beyiba barantana yad'aga haka ta 'karaci ringing d'inta harta tsinke aka kuma kira karo na biyu nanma beyi niyyar d'agawaba, dan ko kallon wurin beyiba, Momy ce ta kalleshi tasa hannu ta goge hawayen dasuka gangaro kan kumatunta tace "Alhj wayarka fa tana ringing, shiru yayi kamar beji maganar datakeba, magana  ta'karayimashu lokacin da kiran wayar ya'kara shigowa karo na ukku "Alhj yakamata ka d'aga wayarnan dan da alama kowaye yadamu daya gayama kowace mgana ce saboda wanda yakiraka dai-dai wannan lokacin 'karfe shidda na safiya yakira baka d'agaba yanace yanata kira kasan maganar nada matu'kar muhimmanci, tana rufe bakinta wani kiran yakuma shigowa karo na biyar, Momy bata jira daddy ba tanufi inda wayar take ta d'auko ta danna ok sannan ta mi'kamai ba musu ya kar6a yakara akunnensa batare daya kalli sunan wanda ke kiranba.


 "Assalamu Alaikum aka fad'a a d'aya 6angaren, me maganar bejira jin abinda Daddy ze fad'aba yacigaba da magana 
"Sunana Ahmad turaki comusioner of police, ina fata dai muna magana da Alhj manair company? 
"Eh dashi kake magana daddy yabashi amsa a ta'kaice.
Zaku iya zuwa babbar headquarter mu ta police domin tabbatar da wata gawa da muka tsinta kota d'iyarkace.

Saurin mi'kewa tsaye Daddy yayi yana yana salati "to shikenan ganinan zuwa bekobi takan Momy ba ya suri key d'in motarsa jikinsa dagashi sai jallabiya, silifas yazura a 'kafarsa yana shirin fita, momy tabiyoshi tana tambayarshi "Alhj lafiya? Beko sauraretaba yawuce hankali tashe.

Fad'awa Momy tayi kan gado tafashe da wani irin kuka me ban tausayi "ya Allah ka bayyanamin Hassana Allah sa duk inda take tana cikin aminci da kariyarka ya ubangiji, wani sabon kuka ya kubce mata.

Daddy na isa headquarter police bayan sun gaisa da comusioner nan yahad'a daddy da wasu police guda hud'u suka nufi babban asibitin dake garin kai tsaye matuare (d'akin ajiye gawa) suka nufa nan aka jawo dorowar da gawar Hussaina take, Daddy na ganinta yafashe da kuka kamar 'karamin yaro, nan ya tabbatarma 'yansandan d'iyarsace lokacin duk kamanninta sun  canja fuskarta ta kunbura ga jini daya gama wanke mata jiki. 

Nan yansandan suka shiga rarrashin Alhj "kayi ha'kuri Alhj inshaAllah zamu tsaurara bincike sai mungano Wanda ya aikata wannan mummunan laifi, dan bincike ya nuna ankashe marigayiyar ne ta hanyar dukan da akayimata aka.

Daddy kasa magana yayi sai kuka kawai dayake, haka aka d'auki gawar Hussaina cikin motar police d'in aka nufi gida da ita.







Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜ญ
[2/2, 9:05 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป


 
Page......................37



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Momy kuwa tun bayan fitar daddy Daga gidan gabanta keta fad'uwa takasa zaune takasa tsaye.

Jin 'karar bud'e get tayi da sauri tatashi tanufi 'kofar fita daga falon zuwan harabar gidan, ganin motar me gidanta tare data police yasa tayi saurin komawa ciki tare da dafe 'kirjinta saboda jitake kamar zuciyarta zata fad'o saboda bala'in fargaba.

Jin annufo falon yasa fad'uwar gabanta ya yawaita, bata ankareba kawai sai gani tayi anshimfid'ar da gawar Hussaina tsakiyar falon, tana kai dubanta gareta taji duk illahirin wasu jijiyoyin jikinta dake aiki sunyi tsaye cak, kafin ayi wata magana sai ganin Momy akayi 'kasa ba alamar numfashi tattare da ita.

Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un Daddy yari'ka furtawa da sauri ya d'auko ruwa ya yayyafa mata, nan akayi nasarar dawowar numfashinta bakinta d'auke da salati.

Nan Daddy yacigaba da yimata nasiha yana rarrashinta da 'kyar yasamu ta nutsu ba abinda take maimaitawa a zuciyarta sai salatin annabi.

Ranar kafin ad'au wani lokaci labarin mutuwar Hussaina ya bad'e gari dandanan gidan Alhj mansir yacika da 'yan'uwa da abokan arzi'ki wasu na zubar da hawaye wasu kuwa sunyi jugum-jugum. Amma duk a tunananin mutane harma da daddy da Momy Hassanace ta mutu.

**                    **                **

Hassana zaune tana duba wani littafi na addu'oi kad'an-kad'an tayi try number Hussaina wai ko Allah zesa tashiga dan tanaso tagayamata Halin datake ciki, amma kamar kullum dai akashe ake cewa.

Jabeer ne yashigo jikinsa a sanyaye. haka kawai yana shigowa Hassana ta tsinci kanta da wata mummunan fad'uwar gaba.

Kallonta yayi ya matu'kar tausaya mata sannan yace "ki tashi yanzu zamuje gida daddy yana nemanmu, jitayi fad'uwar gabanta ya tsananta lokaci guda hawaye ya wankemata fuska a tunaninta jabeer yakai karartane.

Tasowa tayi jiki a sanyaye ta dur'kusa gaban jabeer "dan Allah kayi ha'kuri indai wannan maganarce nayima Al'kawari wlh zan gyara.

Wani irin tausayinta ya'kara mamaye zuciyarsa "a'a ba wannan maganar bace ban dad'e da isa office ba daddy yakirani yace muzo yanzu nidake nikaina bansan ko miye dalilin kiranba, haba tanajin haka wani sabon tashin hankali ya ziyarceta jikinta yafara kyarma kad'an yarage tasaki fitsari dan bako tantama tasan asirinsune ya tonu kan abinda suka aikata itada 'yar'uwarta nasanya jabeer yin *AUREN TAGWAYE* batare da saninsaba, innalillahi kawai tacigaba da furtawa acikin Zuciyarta, ahaka tanufi bedroom ta bud'e wadrope ta d'auko wata doguwar Riga ta canja kayan jikinta sannan tasaka hijab med'an girma wacce ta tsayamata iya gwiwa, plate shoe tasako sannan tafito falo ta iske jabeer na jiranta, yana ganin fitowarta yayi gaba tana biye dashi har gurin mota yabude gurin driver ya zauna sannan itama yabud'emata gidan gaba ba musu tashiga, amma duk illahirin jikinta kyarma yake dan kallo d'aya zakayimata ka tabbatar da bata cikin nutsuwarta.

Ahaka har suka 'karaso 'kofar gidansu tundaga nesa tahango dandazon Al'umma haka yacanjamata tunanani Zuwa wani daban "to wannan iyayen mutanenfa meke faruwane "innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un.

Hankalinta be'kara tashiba saida tashiga harabar gidan nanma cike yake da jama'a maza suna jiran afito da gawa, cigaba tayi da tafiya dai-dai 'kofar dazata sadata da falon gidan taga wasu gun-gun mata zaune sunyi jugum-jugum sai d'aya daga cikinsu ta nuna Hassana tana cema sauran matan "wannan itace Hussainar marigayiyar, d'ayar tace  "oh itace wacce akayima aure kwanakin baya, d'aya tace itacefa Allah sarki mutuwa me yankan 'kauna lalle wannan yarinya tayi rashi Allah bata ha'kuri da dangana.........

Dai-dai wannan lokacin Hassana tanemi numfashinta tarasa sai mutanen dake gurin sukayo kanta anata salati aka kinkimeta akayi ciki da ita.

Dai-dai lokacin kuma aka fito da gawar Hussaina domin kaita makwancinta.





*Anan inso inja hankalin Al'umma akan mutuwa, yanzu abinda aka gane shine da ance wane ya mutu sai mata suje su cika gida wasuma ba dangin iya bare na baba, kuma Alhalin lokacin ana kimtsa gawa irin haka na jawo matsaloli da yawa, da zarar ka mutu 'yan'uwanka da iyayenka sha'kikai ake bu'katar suje ga gawarka bawai mutanen unguwaba, ba'ace kada mutane suje gidan suyi gaisuwaba amma ayi ha'kurin kauda mamacin, mata inajan hankalinku da kunyi gaisuwa ga wad'anda akayima mutuwar kutafi gidajenku shine mafi Alkhairi agareku kada azauna zaman gulma da cin abincin gidan mutuwa. ALLAH SA MUDACE ALLAH KUMA YASA MUCIKA DA IMANI ameen*
[2/3, 10:16 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................38



® _TALENTED WRITER'S GROUP_  _(TWG)_ ๐Ÿ“



Nan fa aka Shiga wani sabon tashin hankali ganin Hassana kwance ba Alamar numfashi tattare da ita, Momy kuka take tama rasa inda zata dosa saboda tsabar rud'ewa.

Sai kusan awa ukku sannan Hassana ta farfad'o lokacin 'Karin ruwane ke shiga jikinta, ahankali tafara bud'e idonta ido biyu sukayi da 'kanwar babanta Haj Uwani tana mata firfita, ganin ta bud'e idonta yasa tafara jeramata sannu.

Bin robar 'karin ruwan dake hannunta tayi da kallo, tunanin 'yar'uwarta tafad'omata arai "yanzu shikenan Hussaina tamutu nashiga ukku, ya zanyi da 'kullallen al'amarin data barni cikinsa, yazanyi in tunkari iyayena da mijin 'yar'uwata da wannan 'kazamin Al'amarin damuka aikata.

Fashewa tayi da wani irin kuka me ban tausayi, tana 'ko'karin tashi daga kan gadon, saurin ri'keta Haj Uwani tayi tare da rarrashinta.

"Kiyi ha'kuri Hussaina dukkan me rai mamacine, addu'a kawai zakibi 'yar'uwarki da ita, dan ita tafi bu'kata akan kome "Allah ji'kan Hassana yakai Haske kabarinta Allah toni asirin wad'anda suka aikata wannan mummunan aiki akanta, Haj Uwani tafad'a tana share hawayen fuskarta.

Hassana kuwa kwance tayi, tayi lamo akan gado tana sauraren yanda Mama Uwani 'Kanwar daddy take kwararo addu'a akanta bayan ita tasan ba itabace ta mutu, amma babu damar tafad'i, hawaye yacigaba da kwarara daga idanunta ba 'kakkautawa. Ahaka Momy tashigo d'akin hannunta d'auke da cup, ganin Hassana na kuka ya 'kara d'aga hankalinta itama kad'an yarage tafashe da kukan da kyar ta rarrashi zuciyarta, ta daure tami'kama Haj Uwani cup d'in hannunta "gashi tunda tatashi 'kara ta daure ko tea tasha kota d'an samu 'karfin jikinta.

Nan Haj Uwani kar6i cup din ta tada Hassana zaune tana 'ko'karin bata tea d'in tana 'kin kar6a da kyar tasamu tasha Rabin cup takoma ta kwanta da tunani barkatai cunkushe a kwalwarta.

        *Bayan sati d'aya*

Hankali yad'an kwanta mutane 'yan'uwa na kusa dana nesa kowa ya koma gida, gidan yarage daga Momy sai Hassana wacce tundaga ranar da'akayi rasuwar tazo bata komaba saboda har yanzu jikinnata ba 'karfi  duk tabi ta rame ta kod'e.

 Washe gari ranar kwana takwas da rasuwar Hussaina Momy da Hassana na zaune, Momy na aikin rarrashinta akan taci abinci dan duk yinin yau batasa kome acikintaba, daddyne yashigo gidan da sallama, Momy ta amsa masa sallamar tare dayimashi sannu da zuwa, kallon Hassana yayi yaga yanda tarame ta kod'e cikin sati d'aya duk ta fita hayyacinta, har cikin ranshi ya tausayamata dan yasan ba karamar sha'kuwa tayi da 'yar'uwar tataba, sai dai al'amarin ubangiji ba ruwanshi da sha'kuwar dake tsakaninka da mutum idan yatashi d'aukar rayuwarsa.

"Hussaina, daddy yakira sunanta.
Gabanta yafad'i sannan ta juyo ta kalleshi tare da amsawa, amma kanta sadde 'kasa dan bata yadda su had'a ido dan gani take idan suka had'a ido da daddy ze iya gane cewa ba Hussaina bace.

Daddy yacigaba da magana "inaso kitashi ki shirya dan munyi waya da mijinki yanzu haka yana kan hanya zezo ya d'aukeki sai kitashi ki shirya kikoma d'akin mijinki kicigaba da biyayya, kinga dai abinda yafaru da yar'uwarki saboda haka kicigaba dayimata addu'a Allah kai haske kabarinta, yana gama fad'in haka ya wuce d'akinshi, Hassana kau fashewa tayi da wani irin kuka tafad'a jikin Momy tana maida numfashi sama-sama.

Hankalin Momy ya masifar tashi ganin yanda Hussana ke kuka ga numfashinta na fita sama-sama, amma ba yanda zatayi dan tasan tunda Daddy yariga ya furta takoma tofa ba fashi saita koma yau d'in, saboda haka jiki a sanyaye Momy tatashi ta taimaka mata tayi wanka, tana fitowa tad'an shafa mai sama-sama sannan tacanja kayan jikinta zuwa wata doguwar Riga, bata dad'e da gama shirinba suka jiyo tsayawar motar jabeer a harabar gidan, kafin jabeer yashigo ciki daddy yafito ya umarci Hassana data tashi sutafi kada ta 6atamai lokaci.

Haka ta mi'ke jiki ba laka tanufi harabar gidan tana tafiya tana waige jitake kamar takoma tasanar da daddy gaskiyar Al'amari amma data tuno da irin zuciyar daddy sai tsoro yakamata, dan tasan tsaf itama ze iya aikata inda 'yar'uwarta tatafi.

Ahaka ta isa gurin motar jabeer na ganin tahowarta yashige mazaunin driver tare da budemata gidan gaba tashiga ya tayar da mota me gadi ya bud'emasu get suka d'au hanya.







Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ‘Œ๐Ÿป
[2/4, 4:46 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................39



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Tun a mota Hassana ke faman kuka har suka iso gida, jabeer nayin parking tafito tanufi cikin gidan dagudu tana 'kara fashewa da kuka, tana shiga falo tawuce bed room tasa key tarufe 'kofa

tarufene dan bata bu'katar jabeer yabiyota yace ze rarrasheta, fad'awa tayi kan gado tacigaba da rizgar kuka Kamar zata cire ranta. 

Tunanin Hussaina yafad'omata arai yanda suke kome tare, ba abunda ke rabasu ko bacci basu yadda yarabasu har tayi aure amma gashi mutuwa tarabasu, zaune tatashi ta d'auko wayarta tana kallon Hotunan dasukayi itada Hussaina lokacin suna gida wasu sabbin hawaye suka kwararo a idanunta, tafara surutai kamar wacce ke magana da wani a kusa da ita tana kallon wani hoto na Hussaina "sister mesa kika tafi kika barni da 'kulallen Al'amarin da bansan yanda zanyi in warwareshiba, Hussaina ina kikaje aka rabaki da rayuwarki, me kikayimasu suka kasheki, ya Allah ka toni asirin kosu waye suka aikata maki wannan abin.

Cillar da wayar tayi gefe takoma kan gadon ta kwanta tacigaba da kukanta, 
Bata tashiba sai 'karfe bakwai da rabi na dare lokacin wani matsanancin ciwon kai ke addabarta, a daddafe tatashi tashiga toilet ta d'auro Al'wala ta rama sallolin da'ake binta daga magrib har isha'i tadad'e tana lazimi kafin tashafa takoma kan gado ta kwanta, tunani barkatai takeyi a zuciyarta tace "ni yanzu yazanyi in fidda kaina cikin wannan sar'ka'kiyar......






     Bayan kwana goma tunda Hassana tadawo gidan jabeer bayan rasuwar Hussaina bata yadda su had'u da jabeer.

Kalacin safe saitaji fitarshi take fitowa tasamu abinda zata sama cikinta, dukda ba wani abincin kirki takeciba hakanan take tutturwa, da rana zata fito tayi abinci tajera a dining sanan ragyara ko'ina na gidan ta share hadda d'akin jabeer d'in, tana gamawa take ibar wanda tasan ze isheta daga lokacin har dare sannan takoma d'aki bakuma Zata 'kara fitowaba sai gobe idan taji fitar jabeer d'in

Tun jabeer na rarrashinta akan tafito ta daina zaman d'akinnan har yaha'kura ya kyaleta ganin tunda yake magiya ko saurarensa batayi sai dai duk ranar dayayimata magana yajiyo sautin kukanta.



: Bayan sati d'aya tana zaune d'aki kamar yanda tasaba tanajin lokacin da jabeer yafita saboda haka da sauri tafito tahad'a abinda zataci, dankali da kwai tasoya sannan tahad'a tea cikin cup tadawo palo ta zauna tafaraci, bawani dad'insa takejiba dan yau tashi tayi da wata irin kasala ga tashin zuciya dake addabarta, ahaka tasamu ta tuttura dan yunwar jinta takeyi, tana gama cin abincin kuwa yafara tu'karta da gudu tanufi toilet tafara she'ka amai, saida ta amayar da duk abinda taci sannan taji sau'ki-sau'ki 

Nan take kuma  wani irin zazza6i yarufeta, tafara   kyarma kan gado tafad'a sannan tajawo wani 'katon bargo ta kudundune dukda uban zafin da akeyi a lokacin.




*kuyi ha'kuri yau namaku typing kad'an, da bazanyiba ma ganin mutane sun matsamin yasa nayi, muhad'u a page na gaba*




Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ
[2/6, 9:28 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................40





® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“




Jabeer be dawo gidan ba sai bayan sallar azahar kamar yanda yasaba dawowa, da sallama yashigo falon kai tsye d'akinshi ya wuce yafad'a toilet yayi wanka danya kwaso gajiya sosai, bayan yafito daga wankan ne ya murzama jikinshi mai sannan ya canja kaya zuwa 'kanana marassa nauyi, falo yadawo kai tsaye dan yakwaso yunwa sosai yasan ze tarar da abinci kamar yanda yasaba.


Falo yadawo kai tsaye ya doshi dining area amma bisa mamakinsa sai yaga wayam bako cokali gurin barantana yasa ran abinci, cike da mamaki yashiga kitchen nanma ganinsa yayi tas ko ina a share a goge ba alamar andafa wani abinci cikinsa, cike da mamaki yadawo falon sannan yanufi d'akin Hussaina nocking yayi ahankali duk da yasan ba bud'ewa zatayiba, hannu yasa yad'an murd'a handle d'in 'kofar da mamaki kawai sai gani yayi kyauren ya bud'e, ahankali yashiga d'akin yari'ka dubawa  inda ze ganta can idanunsa sukayimai tozali da ita tana kwance kan gado ta kudundune a bargo tanata makyarkyata kamar wacce aka she'kama ruwan 'kan'kara, duk zafin da akeyi a garin.


"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un jabeer yafad'a tare da nufar inda take kwance, zama yayi gefen gadon tare da bud'e bargon yana kallonta sannan yakai hannunsa kan wuyanta, jin wani irin zafi yayi rau ajikin nata, "subhanallah zazza6i Kike amma baki gayaminba sai ki zauna da ciwo ajiki, kitashi mutafi asibi,


: Bejira mezata fad'aba yanufi wadrope ya d'aukomata hijab, da kanshi ya taimaka mata ta sanya hijab d'in sannan suka nufi mota da sauri jabeer yabud'emata gaban mota ba musu ta zauna sannan ya zagaya yashigaazaunin driver suka d'au hanyar asibiti.

Bakin wani private Hospital suka tsaya me suna *Allah Bamu Lafiya* dake cikin garin katsina jabeer da kanshi ya taimakama Hassana tafito daga motar suka nufi cikin asibiti, suna zuwa kai tsaye aka bud'emata file sannan aka turasu gurin likita, bayan yan tambayoyi da likitan yayima Hassana itakuma tayimai bayanin duk abinda takeji, nan take likitan ya danna wata 'yar karaurawa saiga wata nurse tashigo, ta rissina gaban likitan cikin ladabi, ya nunamata Hassana "kije da ita kiyimata wannan gwaje-gwajen yafad'a yana mi'kamata wata takarda, "owk sir tafad'a tare da amsar takardar sannan takama hannun Hasaana suka nufi lab, nan aka ebi jini sannan tanunamata toilet tabata wani d'an konkoni na roba ta umarceta datayo fitsari anan, haka Hassana tayo fitsarin takawo sannan takoma kan wani benci Wanda masu jira ke zama ta kwanta ta kudundune cikin hijab d'inta dan har yanzu wani irin sanyi takeji, 


Kusan minti talatin suna jiran result ganin yanda mutane ke 'kara yawa yasa jabeer matsawa kusa da Hassana yace "ko muje inkaiki gidanmu tunda kusane ni sai indawo injira sakamakon dakuma magungunan daza'a rubuta.


'Daga mashi kai kawai tayi, alamar hakan yayimata dan dama ita tamatsu dasubar wannan asibitin ganin yanda mutane suketa zuwa gashi gurin zama ma yana neman gagarar wasu itakuma ga wani irin sanyi datakeji.


 Da taimalonshi suka isa gurin mota, bud'emata yayi tafara shiga  sannan shima yashiga yatshi motar suka tafi, kasancewar ba nisa tsakanin asibitin da gidansu jabeer ba'a d'au wani lokaciba suka iso, bakin 'kofar gidan sukayi parking sannan suka fito, suka nufi cikin gidan Ahankali Hassana take tafiya tana biye da jebeer, yanayi yana waigenta har suka isa cikin gidan suka kwad'a sallama Umman jabeer daga d'aki ta amsa, dai-dai lokacin 'kanwarsa nusaiba tafito daga wanka ta kai dubanta garesu cike da fara'a "Lah Yaya jabeer ashe tare kuke da aunty Hussaina, jin an ambaci Hussaina yasa Umma Fitowa daga d'aki tana masu sannu da zuwa, takai dubanta ga jabeer baka cemin tare kuke.

"Eh wlh mama daga asibiti muke shine nace bari inkawota nan tad'an huta kafin agama gwaje-gwajen daza'ayi.

"Subhanallah, Umma tafad'a meyasameta? Ta tambaya tana 'karema Hassana kallo wacce ta saddar da kanta ta'ki bari su had'a ido da Umma, amma hakan behana Umma tagano wani Abu tattare da itaba, murmushi tayi me d'auke da farin ciki, sannan takama Hannun Hassana suka nufi d'aki tanata jera mata sannu.











Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ‰
[2/7, 10:32 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................41



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(RWG)_ ๐Ÿ“


Jabeer ne zaune gaban likita, saida likitan yayi wasu 'yan rubuce-rubuce sannan yafad'a mashi ainafin abinda ke damun Hassana, sannan yabasu shawarar hanyoyin daza'abi domin kare lafiyarta, 


Nan jabeer yayi godiya sannan ya sayi magungunan da'aka rubuta ya wuce gida.

Da sallama yashigo gidan, zaune ya iske Hassana da kwano a gabanta d'an wake ne Mamanshi tayimata shine takeci dan ba 'karamin dad'i yayimataba,  dai-dai lokacin nusaiba tafito daga d'aki cikin kayan islamiyya kalar ruwan 'kasa, cikin ladabi ta isa kusa dashi "yaya harka dawo? "Eh nadawo nusaiba ina mama take ? "Tashiga nan makwabta zata kar6oma Aunty Hussaina kunun aya, tunda kashigo ni bari na wuce islamiyya dama nafara latti baniso inbar aunty ita kad'ai shiyasa nad'an jinkirta. 

"To shikenan maza kitafi ga wannan kihau napep dan kiyi saurin zuwa yafad'a yana mi'komata d'ari biyu hannu biyu tasa ta kar6a sannan tayi godiya tawuce.

Kujera jabeer yajawo ya zauna gaban Hassana suna fuskantar juna "sannu ya jikin naki,? "Da sauki, tafad'a tana cire Hannunta daga kwanon d'anwaken, buta ta d'auka tanufi bakin maguji domin wanke hannunta, jabeer yabita da kallo har cikin ranshi yake matu'kar tausayamata ganin yanda tarame sai wani uban fari datakara.

Umma ce tashigo da sallama, dai-dai lokacin Hassana tagama wanke Hannunta zata mi'ke Umma tayi saurin kamata ta mi'ke tana ri'ke da ita har kan tabarma datake ta zaunar da ita, tana jeramata sannu a zuciyarta kuma fall da farin ciki ganin takusa samun jika.
Dai-dai lokacin kuma aka kira sallar la'asar saboda haka jabeer besamu damar yin wata magana da maman tashiba yad'auki buta yayi Al'wala ya wuce masallaci.


**              **                  **

Zaune yake gurin wani sha'katawa, gurin ya 'kawatu da itatuwa da flower's masu kyan gani da dad'in 'kamshi, mutane ne kala-kala a gurin wasu mata da mijine da yayansu, wasu kuma saurayi da budurwa, kowa harkar gabanshi yakeyi babu Wanda yadamu da wani, shikam yakasa zaune yakasa tsaye kad'an-kad'an yaduba agogon hannunsa, dan 'karfe hud'u sukayi da ita zatazo nan suhad'u amma gashi har hud'u da rabi kome kama da ita be ganiba.


Wayarshi ya d'auko yayi 'yan danne-danne sannan yakara a kunne, wani abin takaicin cemasa akayi switch off, wani mugun takaici ya lullu6eshi jiyayi kamar ya kwala wayar da 'kasa dan haushi.



 Dai-dai lokacin me napep ya sauketa, sanye take da ba'kin wando pencil da jar riga iyakar cinya, wacce ta d'ameta tafiddo duk wata sura da Allah yayimata, sai wani yala-yalan gyale kalar ba'ki datayi rolling dashi kafarta jan takalmine mai matu'kar tsini, hannunta ri'ke da waya 'kirar iPhone 7 yayinda d'ayan hannun take ri'ke da poss kalar ja, duk illahirin gurin ya buge da 'kamshin tsadadden turarenta, wani 'katon ba'kin glass ne rufe da kwayar idanunta wanda ake kira no respect, cikin takunta na yanga da 'kasaita ta iso inda yake  lokacin yayi zurfi cikin tunanin rashin zuwanta besan ta iso gurinba saida taja kujera ta zauna 'kamshin turarenta ya daki hancinta sannan ya maida dubansa gareta.

"Haba zuby saboda me zaki shanyani anan aka gayaki banida aikin yine tun d'azu nake kiran wayarki gaba d'aya a kashe, cikin tsananin 6acin rai da d'aga murya yake mata magana.

Tashi tayi tsaye tare da d'age bakin glass d'inda ya rufe kwayar idanunta ta d'aga mai hannu "dakata Hafiz karfa kace zaka d'agamin murya, kasani da da yanzu ba d'aya bane, sabodame zakari'kamin shouting a kunne banison hayaniya

Hafiz sakin baki yayi yana kallon zuby yanda take gayamashi magana son ranta, wanda a da koda kud'i aka sakata bazata iya gayamai hakaba.

A zuciyarshi yace lallai dole inyi maganinki zuby, amma a zahiri sai yayi murmushi "sorry abin bekai hakaba yanzu dai zauna muyi magana ta fahimta

Komawa tayi ta zauna ta d'ora 'kafa d'aya kan d'aya tana taunar cingam irinnan gogaggin yan duniya.
"Kingane zuby abinda yasa nakiraki nace muhad'u anan kinga yanzu rabona dake kusan wata biyu kenan kuma kinriga kin sabamin da lallausan jikinki, kin shagwa6ani da shan daddad'ar zumarki 'kauracewarki gareni ba 'karamin cutar dani yakeba yakamata mukoma yanda muke da. 

 
Murmushi zuby tayi me d'auke da rainin wayo, "Hmm Hafiz aini yanzu na wuce ajinka, dan yanzu gaf nake danayi aure, kuma wanda zan aura yafika kyau kud'i wayewa, kai yafika kome wlh.

"Amma waye wannan wanda ze aureki shin besan Halinkiba, ze kwasarma kanshi bala'i "besaniba kuma baze ta6a saniba dan iya sanin da yayimin mutunniyar kirki yasanni kuma ahaka zan bayyanamai soyayyata kuma inada tabbacin ze aureni.

"Kada kaji inata baka labari ban gayama ko wayeba, ba Kowa bane face *JABEER* mijin 'kawata  Hussaina wacce tarigamu gidan gaakiya.

Tana gama fad'amai tasa hannu ta d'auki wayarta da poss d'inta dake ajiye kan table d'in tare da gyara zaman glass dinta a fuska tace kaga tafiyata sai anjima ko...

Tafiya take tana karairaya Hafiz kuwa bin bayanta yayi da kallo yanda take juya mazannai, wani miyau ya had'e 'kutt sannan ya kwalamata kira "Zuby....... A yangance tajuyo ta kalleshi tana wani shu'umin murmushi, hannu yasa Aljihu ya ciro wata agogo ya d'aga mata zaki iya sheda wannan agogon da kuma ranar da kika yaddata.

Wani mummunan fad'uwar gaba taji lokacin data tuno da ranar data kashe Hussaina bayan ta dawo gida tanemi agogon tarasa.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ’
[2/7, 12:25 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................42




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Dawowa tayi ahankali jikinta yayi sanyi, "Hafiz ina kasamu agogona?
"Murmushi Hafiz yayi me cike da samun nasara "Zuby kenan idan ke sammako kikayi wani a hanya ya kwana, kince zaki auri jabeer ko, saboda kinaso zaki aureshi shine kika raba matarshi da duniya, kina tunanin bansan ke kika kashe Hussainaba.

Kyarma Zuby tafara 'kirjinta na dukan tara-tara ta kalli jabeer, sannan ta dake ta nuna ba Alamar tsoro tattare da ita tace "of course, bazan tsaya jayayya dakaiba Nina kashe Hussaina kuma bazan ta6a danasaniba saboda Hussaina tashiga gonatane ta hanyar rabani dakai, Wanda a lokacin banida wanda nakeso bayanka.

Amma yanzu na canja akalata zuwa ga jabeer kuma nasha Al'washin saina aureshi.
Murmushi Hafiz yayi tare da mi'kewa tsaye yayi taku ahankali yazagayo bayan kujerar datake zaune yadafa bayan kujerar sannan yadu'ko saitin kanta yace

"Karya kike Zuby nasan har yanzu kina sona, kuma inada tabbacin babu wani namiji daze maye gurbina a zuciyarki.

Kawai shawarar dazan baki shine :nasan ke mayyar kud'ice kuma nasan badan kome kikeson jabeer ba sai dan kud'insa. 

Idan kinajin shawara me zai hana mu had'a kai inrufa maki asiri idan kin auri jabeer shima ki aikashi inda kika aika matarshi ki kwashe mana dukiyarsa muyi aure mucigaba da jin dad'inmu. Yana gama fad'in haka yadawo kan kujera ya zauna yana fuskantarta.


Wani shu'umin murmushi tayi tacigaba da taunar cingam d'inta sannan tayima Hafiz wani sakaran kallo "baka isaba Hafiz bakuma zeta6a yiyuba kura da shan bugu gardi da kwace kud'i.

Ai dukiyar jabeer tawace ni kad'ai tafad'a tana nuna kanta, 
Murmushi Hafiz yayi sannan ya d'auki wayarshi yayi yan danne-danne saiga duk magan-ganun da zuby tayi ashe yayi recording _Of course bazan tsaya ina jayayya dakaiba nina kashe Hussaina kuma bazan ta6a danasaniba, saboda tashiga gonata_ latsa wayar yayi ya kashe sannan ya maida Aljihu, zaki iya fansar kanki da shawarar danabaki idan kuma kinyi gardama zan mi'ka wannan recording d'in ga hukuma.

Take zuby takashi ta duri ruwa ta dad'e da sanin shu'mancin Hafiz tsaf ze kaita a hukuma kuma ya wanke kansa. "Kada ka damu na amince da shawararka amma dan Allah ka goge wannan rocording d'in, tafad'a tana kyarma kamar wacce akayima wanka da ruwan 'kan-'kara.

"Zan goge kada kidamu fatana kawai mucigaba da harka kamar yanda muka saba.
"Indan wannan ne kada kadamu muje koh.

Owk muje kawai yafad'a, mota suka nufa gidan gaba Hafiz yabud'ema zuby tashiga sannan ya zagaya mazaunin driver suka d'au hanya.

Gidan Hafiz suka sauka ranar sun she'ke ayarsu suduka sun nunama juna sunyi missing d'in junansu.




**              **                  **







Sai bayan sallar isha'i jabeer yadawo lokacin ya iske Hasaana tagama sallah mama ta zubo mata tuwon masara da miyar ku6ewa ga manshanu, nan Mama ta kalleshi "zakaci tuwon ne azuboma "Eh mama ai kinsan tuwo mutuminane, mama da kanta tashiga kitchen ta zuboma jabeer tuwon

Bayan sun kammala ne sukayi haramar tafiya gida, mama ta kalli jabeer "shin ka kar6o sakamakon kuwa a asibitin naji har zaku tafi bakayiman bayanin komeba

"Eh mama na kar6o wallahi ba wani abu bane ke damunta (Malaria) zazza6in cizon sauro, amma ga magun-guna na siyo likitan yace inshaAllah indai tanasha zata samu sauki.

Fara'ar mama tad'an ragu dan ita a tunanunta cikine da Hassana, amma saitaji sa6anin haka "to Allah sauwa'ke Allah maidaku gida lafiya, nan sukayi bankwana suka d'au hanyar gida.

Suna isa sukayi horn megadi yabud'emasu get jabeer nayin parking Hassana tafito da sauri tanufi d'akinta tarufe da key kamar yanda tasaba tayi kwanciyarta, tunanin Hussaina yafad'o mata a rai batasan lokacin data fashe da kukaba,

Shikenan ni yanzu haka zancigaba da zama, gidan yar'uwata ba gidan mijinaba. Ya Allah ka kawomin mafita ina cikin tsaka me wuya.





Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ‡
[2/7, 7:48 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................43




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



*wannan shafin nakine my lovely jikalle ta Halimatu Shu'aibu, momynki na mi'ko gaisuwa gareki sweet dougher d'inta Allah bar zumunci*



Washe gari da misalin 'karfe goma na safe jabeer ne zaune office d'insa da wasu fayiloli yanata faman wasu rubuce-rubuce, nocking d'in 'kofar akayi ahankali, d'agowa yayi ya kalli 'kofar sannan ya maida hankalinsa ga aikinsa, kara nocking akayi karo na biyu, aje biron hannunsa yayi sannan yabada izinin shigowa.

Da sallama tashigo office d'in sanye take da riga da siket na less, wad'anda suka kame mata jiki, sai wani madaidaicin gyale data yafa har saman kai dan kan nata bako d'an kwali, 'kafarta sanye cikin plate shoe, 

Kallonta jabeer yayi daga sama har 'kasa yace "zuby kece tafe da wannan lokacin, 
"Nice tafad'a tana murmushi.
"Bissmillah zauna mana yafad'a yana nunamata kujera.

Ba musu ta zauna tana wani sakar mashi wani shu'umin murmushi, bayan sun gaisa tace "dama zowa nayi inyima gaisuwa dan lokacin da'akayi rasuwar bani gari, gaskiya munyi babban rashi tafad'a tana matsar kwallan munafinci, Hussaina 'kawatace banida tamkarta nayi babban rashi.

A mamakance jabeer yake kallonta, kindai manta Ai Hassanace tamutu ba Hussaina ba.
Wani mummunan fad'uwar gaba zuby tayi lokacin data tuno da shawarar databa Hussaina na cewa Hassana ta zauna maimakinta.
Inkau hakane ba shakka Hassana bata gayama jabeer ba itabace Hussaina idan kuwa hakane akwai aiki babba agabanta.

Jabeer ya kalleta "naji kinyi shiru me kike tunani, firgigi tayi kamar wacce tafarka daga bacci, ah bakome, nizan wuce Allah bada ha'kuri. "Ameen kawai jabeer yace sannan yacigaba da aikinsa.

Jiki ba lakka Tabar office d'in, daga nan gida kawai tawuce zuciyarta cike da tunani barkatai.


 Zuby a d'akinta sai safa da marwa takeyi, tana sa'ke-sa'ke a zuciyarta "tabbas Hafiz shine babban matsalata idanko hakane  dole in d'au mataki kanshi.

Wani mugun murmushi tayi lokacin wanda koni zee bansan ma'anar yinsaba.
Wayarta ta d'auko ta danno sunan Hafiz bugu d'aya ya d'auka "hellow zuby na yadai, akwai labari ne?

"Sosaima kuwa akwai labari me dad'in sauraro, inaso muhad'u a park dinda muka saba had'uwa.
"Owk ba damuwa kamar 'karfe nawa?
"Yanzu-yanzu kome kakeyi ka ajiye kataho dan abari ya huce shike kawo rabon wani.
"Owk ganinan zuwa.

Saurin fad'awa wanka zuby tayi ta she'ka wanka, tana fitowa batare da 6ata lokaciba lotion kawai ta murzama jikinta sannan tasaka irin 'kananun kayan data saba sakawa, tana fitowa bakin titi ta tsaida me napep tagayamai inda ze kaita, cikin mintinan dabasu wuce talatinba ta iso gurin ta sallami me napep, wayarta ta fiddo da niyyar takira Hafiz ta tambayeshi ya isone hangoshi tayi jingine jikin motarsa yana sakar mata murmushi, itama murmushin tayi sannan tanufi gurin wasu kujeru kai tsaye ta zauna, shima Hafiz nan yadawo ya zauna kusa da ita a 'kagare dayaji labarin datazo mai dashi.

Kusan minti biyar da zamansu zuby batayi maganaba, a 'kagauce Hafiz ya kalleta inajinki zuby, na bud'e kunne ina sauraron jin daddad'an labari kinyimin shiru.

Kallonshi tayi daga sama har 'kasa "owk kada ka damu nad'an gajine inaso in huta tukun, bari naje can na kar6o mana drink's mud'ansha konaji sanyi-sanyi,
"A'a kibari in anso mana Hafiz yafad'a yana mi'kewa tsaye, 
"A'a kabarshi kawai zan amso saurin yin gaba tayi dan kada Hafiz d'in yacemata a'a.

Haka ta isa gurin siyar da drink's kwalbar lacasera biyu ta kar6o duk idanun Hafiz kanta dan tsakanin gurin dasuke da gurin siyan drink's d'in ba nisa.

Gurin dawowa maimakin tabiyo hanya street saita kauce ta inda be ganinta,  tad'an jima sannan tayo zagaye tadawo da lemun guda biyu hannunta.

Zama tayi sannan tabud'e kwalba guda tami'kama Hafiz, itakuma tabud'e guda tanasha suna labari nan takeba Hafiz labarin cewa taje office d'in jabeer kuma ya amince da aurenta, wani dad'i yaratsa zuciyar Hafiz, dai-dai lokacin kuma yagama shan lemun lacasera dake hannunsa ya jefar da robar.


 Mi'kewa zuby tayi tsaye tare da kecewa da wata irin dariya tace "anzo gurin kasani Hafiz kwananka ya'kare yau zakayi bankwana da duniya, zuge Jakarta tayi tafito da wata 'yar'karamar kwalba tace "gaga wannan shine ake kira da silent killer, kuma ahine na zubama a lemun dakasha, saboda haka zaka iya zuwa gida karo'ki Umma yafiya kafin ka margaya barzahu, dan baya kisa farat d'aya, ni kaga tafiyata.

Tana gama fad'amashi tami'ke takama hanya tayi tafiyarta.
Hafiz kuwa duk illahirin jikinsa kyarma yake, yasan shu'umancin zuby kome tafad'a zata iya aikatawa, da sauri ya suri makullan motarsa yabar gurin.





Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ“
[2/10, 1:06 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................44




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“





Cikin tsananin rud'ani da tashin hankali Hafiz ya isa gida, falon mahaifiyarsa ya zube yanata mai-maita istigifari, a zuciyarsa yana cewa "wannan bala'i dame yayi kama, gashi yanzu son zuciya yajamin na jefa kaina ga halaka, 'kanwarsa ce tashigo da sallama ganin yayan nata kwance da alama yayi nisa a tunani ga hawaye kwance a idanunsa dan alamu sun nuna besan da shigowar wani mahalu'ki a d'akinba.

Saida ta matso gaf dashi tadafa kafad'arshi "Yaya lafiya kuwa na ganka haka da Alama kukama kakeyi, saurin tashi yayi ya goge sauran hawayen dasuka ma'kale a idonshi ya 'ka'karo murmushin 'karfin hali yace *Bakome  Zee kada ki damu kaina ne kemin ciwo.

"Kuma shine ka zauna a gida, yakamata kaje asibiti, "to 'kanwata zanje jeki shirya saimu tafi tare dan kan yana matsamin sosai bazan iya driving ba, "owk to ba damuwa bari na sanarma Hajiya kafin mutafi, saurin ri'ko hannunta Hafiz yayi kada kije tana bacci kuma kinsan doctor yahana atasheta idan tana bacci, muje kawai idan mundawo mun gaya mata.
A harabar gidan suka bud'e mota suka shiga Zee ke driving Hafiz kuma na zaune gefenta lokacin yaji cikinsa na juyamasa, ahankali ciwon ke gaba, zee kuwa hankalinta ya matu'kar tashi ganin yanda yayan nata ke magowa gashi har wani kumfa yafara fitowa a bakinsa, wani irin mahaukacin tu'ki tari'kayi dan ikon Allah kawai yakaisu asibitin, suna Isa aka kar6eshi Emergency aka nufa dashi, nan lokitoci suka rufa akanshi, yayinda zee ketai kai komo a bakin 'kofar d'akin da aka shiga dashi tanata sharar hawaye dan ganitake kamar za'a fito acemata Hafiz ya mutu dan yanda aka shiga dashi ba alamar rai tattare dashi.


          *washe Gari*
Da misalin 'karfe goma na safe, Zuby na kwance kan gadonta da waya hannunta tana chat a wani tambad'add'en group data bud'e maza da matane aciki ba abinda ake a group d'in sai maganganun batsa da tura  blue film da sauransu, tana chat din ta Lula duniya tanayi tana matse 'kafafu dan tsabar jaraba, da kuma sauraron voice message d'inda wani tsagera a group d'in yaturo wanda shima Admin ne a group d'in. 

ganin wayarta ta tsaya cak tasan kirane ze shigo, tun kafin kiran yashigo tafara buga uban tsaki dan ganin za'a katse mata jin dad'i, amma da mamakinta sai taga number Hafiz a firgice tami'ke tsaye, sai lokacin tatunafa tasaka mashi guba a lemu kuma yasha tasan ba tantama bekwana da raiba, to amma kuma taya aka kirata da number shi.

Tana cikin wannan tunanin har kiran ya tsinke, batare da 6ata lokaciba aka kuma kira karo ba biyu, jiki a sanyaye ta danna ok sannan takara a kunnenta.


 "Hello" Zuby tafad'a cikin muryar fargaba.
A d'aya 6angaren Zee tafashe da kuka tare da cewa "Zuby koh?
Zuby ta amsa da "Eh nice amma wacece ke?
Zee ta'kara fashewa da kuka, sannan tace "ni 'Kanwar Hafiz ce naga kece mutum ta 'karshe da kukayi waya dashi jiya, cuma naga call log d'insa duka sunanki yafi yawa da Alama akwai sha'kuwa tsakaninku shine nakiraki in gayamaki jiya da dare Allah yayima Hafiz rasuwa.

"What Zuby tafad'a kamar tana cikin irin firgicinnan, sannan tadoka uban salati "Allah Sarki Allah ji'kan Hafiz, 
"Ameen" Zee ta amsa kafin ta tsinke kiran.

Zuby kuwa tana kashe wayar rawa tafara takawa tana rera wa'kar ado gwanja inda yake cewa _Me nemam jini yaje kwata, niko bani zuwa bikin daba mata, mata.....mata....._ ta'karashe wa'kar tana nuna kanta "saini zuby duk wanda yaja dani yajishi kushewa, wata shegiyar dariya tayi sannan tafad'a toilet ta she'ka wanka.


Tana fitowa ta tsaya gaban mirror ta watsa wani matsiyacin make up a fuskarta na marassa mutunci, wasu watsatatsin kaya tasaka dan basuda maraba da shigar arna.

Kai tsaye gidan jabeer tayima tsinke, tana isa me gadi yayimata sannu da zuwa ta wuce dan yasanta kwanaki tana yawan zuwa gidan.

Hassana kuwa ganin tad'anji 'karfin jikinta yasa yau tashiga kitchen tagama girki tana d'aukowa daga kitchen tana jerawa kan dining, tagama jera kome sanan ta tafi da niyyar takoma d'akinta dan tasan jabeer yana gab da dawowa kuma bataso yadawo ya isketa a falo.

Ido hud'u sukayi da zuby wacce ko alama bataji lokacin data shigoba, ba 'karamin fad'uwar gaba Hassana tajiba dan ganin zuby tsaye fuskarta ba fara'a ko kad'an.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ˜œ. *Kwana biyu kunjini shiru wlh yauma da ciwon kai natashi, atayani addu'a, amma idan naji sau'ki zan 'kara maku ko page d'ayane zuwa anjima*
[2/11, 9:05 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................45



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“


*Ido Hud'u sukayi da Zuby wacce ko alama bataji lokacin data shigoba, wani mummunan fad'uwar gaba Hassana taji dan ganinta tsaye bako far'a fuskarta kamar bata ta6a dariyaba*

Dakewa Hassana tayi duk da tsanananin fad'uwar gaban datakeyi, tayima Zuby sannu da zuwa.

Ko kallonta Zuby batayiba ta 'karaso cikin falon da takalminta da kome ta wuce kan kujera ta zauna ta d'ora 'kafa d'aya kan d'aya tana jijjigasu.

Ba 'karamin 'karfin Hali Hassana tayiba gurin d'auko lemu daga cikin pridge tahad'o da cup d'in glass ta ajiye gaban Zuby tana fad'in bismillah ga lemu.

Wani matsiyacin kallo zuby tabita dashi, sannan tayi murmushi "kinga ba wannan yakawoniba zowa nayi inyimaki ta'aziyyar yar'uwarki data mutu.

"Eyyah Hassana wai, Hassana tafad'a jikinta na kyarma.
Zuby tayi dariya, "wacce Hassana kuma? Husaaina dai, 
"Innalillahi kawai Hassana ke mai-maitawa cikin zuciyarta ganin da alama zuby tasan kome.

Zuby ta tsiyaya lemu ta kur6a sannan ta ajiye, kafin tacigaba da magana.

"Hassana yau nazo ingayamaki abinda kike zaton ba wanda yasani Hatta da iyayenki, 
"Kina Zaune da mijin yar'uwarki amatsayinta, zaman me za'a kira wannan, zaman dadiro ko karuwanci..... Hmm.......

Hassana tunda Zuby tafara magana wani irin gumi ya karyo mata, zufa ta jiketa dukda sanyin a.c daya gauraye d'akin.

Tayi 'karfin halin cewa "Haba Zuby wace irin magana kike fad'i haka kamar baki sanniba, nicefa Hussaina 'kawarki 'yar'uwatace Hassana ta mutu baniba..........


"Dakata Hassana Zuby tafad'a cikin d'aga murya, "kina tunanin bansan komeba, to bari kiji ingayamaki abinda ke kanki baki saniba.


"Nice nan naba Hussaina shawarar ki zauna a matsayinta kafin tadawo daga inda zataje, nasan tayimaki 'karyar zataje biki, Hmm to ba wani bikin dataje nasan kinsan tsohon saurayinta Hafiz, to wurinshi taje, nikuma a duniya banida wanda nakeso sama da Hafiz, nayi matu'kar farinciki lokacin da Hassana ta gayamin anyimata aure   , saboda nasan hankalin Hafiz ze karkato gareni, amma wani abin takaici dukda aurenta bata rabu da Hafiz ba.

Ban 'kara shiga tashin hankaliba sai ranar danazo gidannan Jabeer yayimin kyautar ma'kudan kud'i, kuma sai naji zuciyata ta karkata gareshi. 

Hakan yasa nabata shawara akan tanemi ki zauna gidannan amatsayinta dan tasamu damar zuwa gurin tsohon saurayinta Hafiz, kamar yanda tagayamin yanaso su had'u, yayinda nikuma nayi amfani da wannan damar na rabata da duniyar dan insamu in mallaki jabeer, 

Cike da tashin hankali Hassana ke nunan Zuby "dama kece kika kashe Hussaina.?

Zuby tayi murmushi "ki dakata mana, me kikeci nabaka na zuba, yanzuma dana gaya maki aiba matsar bakina kikayiba.

Cikin tsananin tashin hankali Hassana tace "Allah ne ya matsi bakinki kuma sai kinyi danasani, zuby batabi ta kantaba tacigaba da kora mata bayani.


"Hmm nayi tunanin mutuwar Hussaina zatasa ki tona kome ki koma gida, nikuma da haka insamu damar auren jabeer. 

Tami'ke tsaye tad'anyi taku biyu zuwa ukku sannan tacigaba da magana "Ranar danaje office d'in jabeer da niyyar inbayyana mashi son danakemashi sai ya nunamin aishi ba matarshi ce tamutuba.

Hmm inajin haka nasan baki fad'i gaskiyaba, kuma kincigaba da zama a matsayin matar jabeer, saboda haka ina baki shawara daki gaggauta tonama kanki asiri kuma kibar gidannan, nice yadace nazauna gidannan koda ban auri jabeer ba, tafad'a tana nuna kanta.

Tana gama fad'in haka tatafi da niyyar barin gidan har takai bakin 'kofa ta dawo tace kuma kada ki kuskura ki gayama wani maganganun dumukayi domin yin hakan barazanace ga rayuwarki, idan kuma bahakaba kema zakibi yar'uwarki inda taje.

Zuby natafiya Hassana tafad'a d'aki tasa key tarufe tafara rizgar kuka tana had'a kayanta cikin trolley, dan wani mugun tashin hankali tashiga Wanda tunda take duniya bata ta6a Shiga irinsaba.









Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„❤
[2/12, 8:52 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................46



Da misalin 'karfe ukku dai-dai jabeer yashigo gidan, kai tsaye d'akinsa ya wuce ya watsa ruwa ya canja kayan jikinsa Zuwa marassa nauyi, sannan yafito zuwa falo dan yaga yau da Alama akwai abinci gidan.

Zama yayi kan dining yazuba macaroni jalouf da Hanta, yanaci abincin nakaimasa karo, saida yaji ba sauran guri a cikinsa sannan yanufi pridge ya d'auko lemu ya tsiyaya a cup yasha , yajima zaune kan dining yana danne-danne a wayarsa kafin yatashi yakoma kan kujera da remote control hannunsa yana 'ko'karin kunna tv yajiyo sheshshekar kuka daga d'akin matarsa, saurin ajiye remote d'in yayi yanufi d'akin dukda yasan idan zeyi juyin duniyan nan da wuya ta bud'e barantana kuma tafad'a mashi matsalarta.

Nocking yafarayi ahankali kafin yakira sunanta, "Hussaina ki bud'e mana bekamata ace ki kulle kanki a d'akiba kuma kina cikin damuwa waye zaki fad'awa kiji dad'i.
Ga kuma jikin naki har yanzu be gama warwarewaba.


Jin maganarsa yasa ta'kara fashewa da kuka, da kamar bazata tanka ba barantana ta bud'e amma sai wata zuciyar tabata shawarar ta bud'e kawai.

Haka tatashi jiki ba laka ta bud'e 'kofar, ganin yanda idanunta suka kad'a sukayi ja, ya tabbatarmashi da ta dad'e tana kukan, wani irin tausayinta ya dira a zuciyarshi, kama hannunta yayi suka koma cikin d'akin ya zaunar da ita gefen gado sannan shima ya zauna dai-dai wannan lokacin kuma idanunsa suka sauka kan trolley data had'a kayanta ciki.

Juyowa yayi ya kalleta da mamaki a fuskarsa, yace "wannan jakar kayanfa lafiya dai.
Shiru tayi dan batasan irin amsar da zata bashiba.
Saida yakuma tambayarta karo na biyu tare da ru'kota yana 'ko'karin had'a jikinshi da nata,

Saurin kwacewa tayi tare da mi'kewa tsaye tafashe da wani sabon kukan, tana ja da baya kamar tana tsoron jabeer d'in.

Da mamaki shima ya mi'ke yana tunkararta "Haba Hussaina danmi kike guduna baki 'kaunar inta6a jikinki ko kad'an amatsayina na mijinki...........


"Kaiba mijina bane jabeer, haka kuma niba matarka bace, matarka ta mutu tsawon wata ukku dasuka wuce, 

"Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un jabeer yafad'a "Hussaina anya kina cikin hayyacinki kuwa, nine yau zakice ba mijinkiba, 
ba shakka lallai 'kila kinfara irin shaye-shayennan na zamani.......

"Ko d'aya jabeer ban ta6a shan komeba, kuma dukkan abinda nafad'ama cikin hankalina nake......

Yanzu zanbaka labarin abinda baka saniba, koda kuwa yin hakan nima ze zama 'karshen rayuwata kamar yanda 'yar'uwata tabar duniya.

Wani sabon kuka tafashe dashi, saida tayi me isarta tayi shiru dan kanta batare data samu me rarrashintaba, saboda jabeer yariga ya shiga wani hali, so yake kawai yaji asalin gaskiyar abinda tafad'a wanda zesa ya yarda cewa ita ba matarshi bace kamar yanda tafad'a.

Nan ta kwashe labarin abinsa suka ahirya tsaf da Hussaina lokacin tana raye, na zamanta gidan amatsayin Hussainar wanda daga tafiyarne bata dawoba sai dai aka kawo gawarta, amma bata gaya mashi wacce takashe Hussainarba, sannan kuma bata gayamashi cewa gurin tsohon saurayinta tajeba, tadai gayamashi taje bikine kamar yanda ita Hussainar tagayamata.

Saukar wani wawan mari taji a fuskarta, wanda har saida taga wasu taurari, dafe kuncinta tayi ta zube 'kasa tana kuka,

Shima jabeer d'in hawaye yake, yarasa inda zesa kanshi, innalillahi kawai yake mai-maitawa, yana fad'in *Allahumma ajirni fi masibati wa khalibli khairan minha* 

"Hassana kin cuceni, kinsa na aikata abinda banta6a aikatawaba, amma ai Allah yana gani batare da sanina na aikataba, komiye kece sila.

Hassana dai bata 'kara maganaba tun marin dayayimata kuka kawai take tana dana sanin amincewa da 'kudirin 'yar'uwarta.

A fusace jabeer ya d'auki trolley data had'a kayan yakai mota, sannan yadawo ya figeta itama ya bud'e motar yajefata kamar wasu kayan wanki, sannan yatayar da motar yafara dokama megadi horn, da gudu yazo ya bud'e masu get jabeer ya kwashi hanya da gudun tsiya.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ’ž
[2/12, 12:46 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................47



® _TALENTED WRITE R'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“


Wani mummunan fad'uwar gaba Hassana tayi lokacin dataga jabeer yayi parking cikin harabar gidansu, amma a zuciyarta saitaji ta dake akan kome ze faru 'kara ya faru da zaman datake, wanda ita kanta batasan makomarsaba.

A fusace jabeer yafito daga motar sannan ya bud'e but ya d'auko trolley yanufi cikin gidan beko kalli inda takeba.

Da sauri tabi bayanshi tana sharar hawaye har tana had'awa da d'an gudu-gudu.

Momy da daddy suna zaune falo suna kallon labarai a tashar aljazeera, suka jiyo sallamar jabeer, daddy ne ya amsa yana 'ko'karin fita yaga jabeer d'in yashigo janye da trolley, komawa yayi ya zauna yana kallon jabeer cike da mamaki harya 'karaso yasamu guri ya zauna dai-dai saitin 'kafar Daddy yana matsar kwalla.

Cike da alamomin tambaya Daddy ke kallon jabeer, Momy ma da alama hakanne a fuskarta.

Suna shirin tambayarsa saiga Hassana tashigo da kuka share-share a fuskarta, kamar wacce aka jeho tafad'i gaban Momy da Daddy tana cigaba da kukanta.

Daddy ne yayi 'karfin halin tambayarsu "lafiya meke faruwa kukazo haka birkice, wani kuka Hassana ta'kara fasawa dan tasan yau kashetane kad'ai Daddy bazeyiba, amma ta kwammace hakan da zaman datake a gidan jabeer.

Suduka ba wanda yayi magana, shima jabeer d'in hawayene ke zarya a kumatunsa, yama rasa ta inda ze gayama Daddy abinda ke faruwa.
Daga 'karshe dai yayi 'karfin hali ya kalli Hassana yace "ki maimaita masu abinda kika fad'amin.


Daddy ya watsa mata wani kallo wanda yasa saida Hantar cikinta ta juya, sannan tayi saurin saddar da kanta tana hawaye, dan tasan babu wasa ko kad'an tattare da Daddy saboda haka batare da 6ata lokaciba ta fayyace masu kome kamar yanda tafad'ama jabeer kafin suzo nan.


 Lokaci d'aya Momy da daddy suka saka salati, kafin Daga bisani d'akin yayi shiru bakajin kome sai sheshshekar kukan Hasaana, wacce jira take kawai taji anrufeta da duka, dan tasan ta caccanci abinda ma yafi haka.

Duk zafin Daddy da d'aukar matakinsa kan abu, yau kasa koda motsi yayi, sai Momy ce tayi magana "Amma Hassana baki kyautaba, itama abinda kawai ta iya fad'i kenan tayi shiru.

Mi'kewa daddy yayi tare da d'aukar makullan motarsa ya kallesu yace "kutaso ku dukanku ku sameni a mota, yana gama fad'i yayi gaba da sauri yabud'e motarshi yashige zuciyarsa cunkushe da ba'kinciki da takaici.

Minti biyar ba'ayiba sai gasu sun fito, gidan gaba Daddy ya umarci Jabeer ya zauna Hassana kuma da momynta baya.
Sannan daddy ya tayar da motar, Malam bala me gadi yabud'e masu get da sauri yana masu Allah kiyaye.


**              **                 **


Zaune suke gaban wani dattijon mutum Wanda kallo d'aya zakayima fuskarsa ka tabbatar da kamala da ilimi tattare dashi, dan ya ajiye sunnah a fuskarsa (gemu) bayan sun gaisa Daddy yayi Mashi bayani dukan abinda ke tafe dasu.

Malam Kasim yayi matu'kar mamakin jin wannan abu daya faru amma dayake shi addini me saukine kuma ya kawo yanda za'a warware kowace matsala saboda haka yafara yimasu bayani bayan yayi addu'a da salatin annabi (s.a.w)


"To kamar yanda kuka Sani tunda ita wannan yarinya dama ba matarsa bace bamu bu'katar ace sai yasaketa, amma tunda har wani abu na mu'amalar auratayya yashiga tsakaninsu, to zatayi istibira'i idan tagama zata iyayin aure.
*(Istibira'i yana nufin zama da wacce tayi zina takeyi a gida na tsawon wasu watanni batare data 'kara kusantar zinaba, dan ta tsarkake kanta kafin tayi wani auren)*

Nan sukayima Malam godiya sannan suka koma gida, Hassana tayi matu'kar mamakin yanda iyayenta suka kar6eta batare da sun nuna matsanancin fushi akantaba.

Tayi mamakin yanda Daddy ya umarci data wuce d'akinta tayi wanka kuma tacigaba da istigifari domin shi Allah gafurun rahimunne.

Haka tawuce d'aki sukuku kamar kazar da kwai ya fashemawa a ciki.
Tana shiga d'akin kuwa tafad'a kan gado tafashe da wani sabon kuka dan tunowa datayi da Hussaina wacce tare sukayi rayuwa a d'akinnan amma yanzu gashi bata raye.
Zuby tafad'o mata arai, a zuciyarta ta rin'ka banka mata Allah ya isa dan duk halin datashiga itace sila, sannan kuma taraba 'yar'uwarta da duniya.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ›
[2/19, 7:07 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................48




® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



             *Bayan Sati Biyu*

Zaune yake yahad'a uban tagumi duk abubuwa sunbi sun dagulemai, ba abinda yake tunani sai tsawon lokacin da suka d'auka suna zaman aure da Hassana wadda duk  a tunaninsa Hussainace wai ashe Hussainar ce ta mutu ba Hassanaba, wasu siraran hawaye suka zubo kan kumatunsa, beyi 'ko'karin gogewaba haka yabarshi yanata zuba wani na bin wani.

Sallamar da ake dokawa daga bakin 'kofar falon ce tasa yayi saurin goge hawayen dake fuskarsa tare dayin 'karfin halin amsa sallamar.

Yauma kamar kullum sanye take cikin irin matsiyatan kayan data saba sanyawa, duk illahirin surar jikinta a bayyyane take.

Da mamaki yabita da idanu yana kallonta ganin wani shu'umin murmushi datake sakarmai, kafin yayi magana ta ida 'karasowa cikin falon ta zauna kan d'aya daga kujerun dake zagaye da falon sannan ta d'ora 'kafa d'aya kan d'aya kafin tafara magana.


"Da farko dai jabeer ina 'kara yima ta'aziyyar matarka Hussaina data rigamu gidan gaskiya, sannan kuma ina jajantama game da cin amana da suka 'kullama tsakaninta da 'yar'uwarta sukasa kayi *AUREN TAGWAYE*  batare da saninkaba.

Ta numfasa sannan taci gaba da magana "kada ka damufa da wannan Allah be ta6a kama bawansa da laifin da besaniba _(niko zee nace kaji su zuby kamar ansan Allah)_ 

Jabeer kuwa tunda tafara surutunta 'kala be cemataba ita kad'ai keta zuba shikuwa binta kawai yake da ido.

Tasowa tayi daga inda take zaune tana wani girgiza tana rangaji harta 'karaso gabanshi ta dur'kusa.
"Jabeer akwai wata magana danazo da ita amma bansan ya zaka d'auketaba.
Tayi shiru tare da zubamai mayataccin idanunta alamar tanason jin tabakinsa kafin tacigaba.


"Ina jinki kawai jabeer yabata amsa atakaice sannan tacigaba damagana,

"Jabeer na dad'e ina dakon soyayyarka acikin zuciyata tun kafin ka auri Hussaina, ganin tana aminiyata yasa na ha'kura ban ta6a nunamaba, domin masu iya magana sunce ana barin halak kodan kunya, amma yanzu tunda babu ita, kaga zaka iya aurena in mayema gurbinta, kuma..........

Saurin d'aga mata hannu yayi "dakata dan Allah zuby, yafad'a cikin 'kunar rai, dan tunda tafara magan-gamunta jiyake kamar tana watsa mashi garwashin wuta acikin zuciyarsa.
"Kada ki kuma tunkarata da wannan maganar danni yanzu ba abinda ke gabana kenan ba, zuby kisani na tsani rayuwa da wata mace a yanzu saboda haka kada kisa ran zan iya rayuwa dake.......

Murmushi tayi  "Hmm nasan ciwon abinda Hussaina tayimakane yasa ka furta wannan kalamin, amma mata ai mune abokanin rayuwa, babu namijin da baya bu'katar mace kusa dashi matu'kar yanada cikakkiyar lafiya.....


"Fita dan Allah, ki fitarmin daga gida kina 6atamin lokaci, yafad'a yana nuna mata 'Kofa, 

Murmushin takaici Zuby tayi a zuciyarta tace "wannan wane irin zuciyane dashi tun bayan wata biyu dasuka wuce naketamai hannunka me sanda dan yagane ina sonshi, gashi har yau na bud'a baki na gayamashi sirrin dake raina amma gashi yana nuna halin ko inkula akaina, tabbass akwai aiki babba agabana.......


"Get out, maganar jabeer ce tadawo da ita daga dogon tunanin datake, wacce har saida tayi 'yar'karamar razana, sannan ta kalleshi ta jefeshi da murmushin takaici kafin tasa kai tafice daga gidan.


Tana fita yabi bayanta, megadi na zaune bakin aikinsa, ganin jabeer yasashi tasowa yana mashi barka da fitowa, fuska ba annuri jabeer yace "daga yau idan ka kuma barin wannan yarinyar shigowa gidannan bakin aikinka...

Me gadi yayi saurin dafe 'kirji tare da fiddo idanu waje, jin an ambaci aikinsa, jiki na kyarma yace "inshaAllah ranka ya dad'e hakanma bazata faruba.
Be tsaya sauraronsaba yakoma cikin gidan, yana Shiga falo yafad'a kan kujera, tinanin rayuwar da yayi da Hassana tafad'o mashi a rai.














Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿง
[2/19, 8:15 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................49



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Tundaga wannan lokacin Zuby ke zarya gidan jabeer amma koda wasa me gadi baya barinta Shiga, idan zatayi juyin duniyar nan be barinta, data gane haka saita koma zuwa office d'insa, nanma Haka ya gargad'i ma'aikatan gurin da kada akuma barinta tana shigowa, haka kuwa akayi dan akwai ranar datazo tundaga bakin get megadi yahanata shigowa, tayi magiyar tayi duk iya dabararta amma yahanata, kawai saita samu guri ta zauna tana kallon masu shiga da masu fita har bayan azahar bataga fitowar jabeer ba sai gurin 'karfe ukku sannan motarshi tafito, hannu rafara d'aga mashi Alamar ya tsaya, shi kuwa bemasan tana gurin ba.

Ganin be gantaba yasa tayi saurin tsaida me napep tanunamashi motar jabeer tace yabi bayanta,

 Shikuwa besan tana binsaba, kai tsaye hanyar gidan iyayensa yanufa, dai-dai 'kofar gidansu yayi parking sannan yafito duk kan idanunta ya gaggaisa da mutanen dake gurin sannan yashige gidan nasu.

Bata fito daga napep d'inba wani yaro yazo wucewa takirashi, take tambayarsa ko nanne gidansu jabeer?

Yaron yabata amsa atakaice sannan ya wuce, nan ta umarci me bapep daya kaita gida tagaya mai unguwar suka d'au hanya.


        *Bayan kwana biyu*


Zuby tsaye bakin titi jikinta sanye da riga da zani na atamfa wanda rabon datasaka kaya irin wannan harta manta, sai kuma madai-daiciyar hijab d'inda tasanya wacce ta sakko mata har iya gwiwa.


Me napep ta tsaida, sannan tafad'a mashi inda ze kaita, suna isa ta hango motar jabeer a 'kofar gidan haka ya tabbatar mata da yana cikin gidan, zaure ta tsaya tana fargabar shiga amma haka ta dake tayi ta maza tayi sallama, Maman jabeer dake duke bakin gurin tana alwala ita ta amsa sallamar.


 Cikin ladabi zuby tashiga gidan, Maman jabeer tabita da idanu da Alamar tambaya tattare da ita dan bata ta6a ganin zuby ba.

Ganin yanda Zuby ke kakkare fuska da Alamar jin kunya yasa Maman jabeer d'in tayimata iso har d'aki, bayan sun gaisa take tambayarta "yarinya bangekiba, 

Murmushi Zuby tayi "dama jabeer ne yace ze kawoni mu gaisa, to shine mukayi waya nake fad'amashi inanan gidan yayata nan 'kasan layinku sai yake sanarmani ai yana nan gidan in'karaso mu gaisa, takare maganar tana saddar da kanta 'kasa alamar kunya, dan tunda tazo bata yarda sun had'a ido da Maman jabeer d'inba.

Aiko Maman jabeer najin haka ta fahimci inda zancen yadosa, wani irin farin ciki ya lullu6eta, dama kullum fatanta be wuce jabeer d'in yayi aureba.

Kusan minti sha biyar Zuby na zaune tana jiran ko jabeer ze shigo amma be shigoba, hakan yasa tayi sallama da mama tace zata tafi.

Mama tace "tun yanzu baki bari jabeer d'in yashigo masallaci yaje, cike dajin kunya  Zuby tace "ba kome mama sauri nake wallahi islamiyya zani nagama har lokacin yafara wucewa.

To ki gaida gida ki gaida mamanki kinji, "to zasuji inshaAllah tafad'a sannan ta fice daga gidan.

Bakin 'Kofa suka had'e da jabeer yana 'ko'karin shigowa gidan, ganin Zuby tafito daga gidan ba 'karamin tayar mashi da Hankali yayiba, 

"Zuby meya kawoki gidanmu,? Ya tambayeta yana 'karemata kallo dan ba 'karamin kyau shigar datayi tayimata ba, murmushi tayi tace "meko ze kawoni idan banda tsananin so da 'kaunar danikema.

Dur'kusawa tayi gabanshi idanunta na zubar da Hawaye, "Dan Allah jabeer ka taimakeni ka taimaki rayuwata, wallahi ina sonka ina 'kaunarka tsakani da Allah, nasan kasan zafin so, kasan rad'ad'in so, dan Allah kada kacema ummanka baka sona, dan nasamu kar6uwa a wajenta d'ari bisa d'ari dan Allah kaima ka kar6eni kamar yanda ta kar6eni.


Ganin yanda take kuka tana mashi magiya gashi hartasa hankalin mutanen gurin yafara dawowa kansu yasa wani irin tausayinta ya dirarmai a zuciya besan lokacin daya kama hannuntaba yabud'e mota ya sanyata sannan shima yashiga suka d'au hanya.
 
Tunda suka tafi ahanya yake aikin rarrashinta, amma ta'kiyin shiru saida ya amsamata daya amince ze aureta, wani irin dad'i ya lullu6eta, tunnan tafara zumud'i tana sanar mashi da bata son asa bikin nesa idan sonsamune ayi kome nanda wata biyu.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ‘๐Ÿป
[2/19, 9:42 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................50



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



        *BAYAN WATA UKKU*

Hidima ta kankama sosai dan ahalin yanzu saura kwana goma d'aurin auren jabeer da Zuby, 6angaren jabeer be wani farinciki dan jiyake kamar tilastashi ake auren zuby amma ko kad'an babu dai-dai da kwayar zarra na sonta acikin zuciyarsa, 

Ita kuwa Zuby ta dad'e da sanyama ranta zama matar jabeer, tuni tafara tsara yanda za'a gudanar da program d'in bikin itada 'kawayenta, maganar gayya kuma ta dad'e da gama gayyato duka abokaninta maza da mata, program kusan kala bakwai ta tsara za'ayi a cewarta yanzune jabeer zeyi aure na kece raini saboda haka sati guda cif za'ayi ana gabatar da shagulgulan auren.

**                **                  **

Hassana ce kwance d'akinta, duk abin duniya yabi ya dameta ba abinda take tunani sai tsawon lokacin data d'auka gidan jabeer, cikin wannan zaman dasukayi ta la'kanci halayensa da dama ciki kuwa hada tsananin ha'kurin dake gareshi.

Juyi tayi ta gyara kwanciyarta zuwa rigin-gine ta 'kurama silin d'in d'akin ido tsananin so da 'kaunar jabeer na 'kara mamaye zuciyarta.

Wani 'kawataccen murmushi tayi, sannan tatashi zaune ta d'auko wayarta chat ta hau tana dubawa, wanda rabon data hau and'au lokaci me tsawo.

Best group d'inta tafara shiga na *Ciwon 'ya mace* tana duba d'umbun message d'inda ta taras kwatsam idanunta sukayi kaci6is da hotunan wasu amarya da ango da aka turo ana gayyatar duk wanda yasamu damar halatta, ganin yanda aketa maganar bikin da kuma yanda ake fad'in kalaluwan program d'inda za'ayi yasa taji tana sha'awar bud'e hotunan amarya da angon dan taga yayan wani hamshakinne ake gagatawa haka.

"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un tashiga furtawa lokacin da idanunta sukayimata kaci6us da hoton jabeer da zuby.


Take wani irin gumi ya karyo mata, a hargitse tami'ke ta sanya hijab d'inta sannan ta sanya ni'kaf da safar hannu data 'kafa, sannan ta 'kara d'auko wayarta ta 'kara kallon hoton jabeer da zuby ta 'kara kallo Sannan tafara magana kamar Zuby na jinta "'karya kike Zuby, wallahi 'karyarki tasha 'karya baki isa ki kashemin 'yar'uwaba kuma ki auri mijinta wallahi saina d'au tsatstsauran mataki akanki.
Tana gama fad'in haka tafice daga gidan batare data nemi izinin Momy ko Daddy ba.


 **               **                 **

Zuby kuwa kud'i ta amsa masu yawa daga hannun jabeer tasiyo kaya kusan kala goma wad'anda zata sanya gurin bikin, kowane kaya da jakarsa da takalminsa,  yau sukayi da telanta zataje kar6ar d'inkunan saboda haka waya tafarayimashi ta tambayeshi ko ya'karasa, yacemata yagama ita kawai yake jira.

Wata 'katuwar hijab tasaka sannan tafita, dan tunda tasamu tashawo kan jabeer ta daina shigar banza, koma Tayi saita saka 'katuwar hijab.

Minti ashirin ya sadata da shagon *USMAN FASHION*  Wanda ta yarda kuma ta amince da d'inkinsa dan babu wani tela dazemata d'inki taji dai-dai idan bashiba, ya kware a d'inkin mata, danshi baya d'inkin maza, lokacin data shiga shagon saida Hussaina tafad'o mata a rai dan itace ta nuna mata shagon telan sune nan daddy ke kawo masu d'inkinsu duka harda na momy.

*Wannan tallace ga babban tela USMAN FASHION shagonsa nanan cikin garin katsina sabon layi bayan tsohuwar refabulik Hotel, d'inkin mata zallah na Zamani atamfa, material, shadda,  yakeyi, duk me bu'katar 'karin bayani zata iya tuntu6armu ta wannan no*      ๐Ÿ‘‡๐Ÿป

07037112229

*Usman Fashion yataso me maida tsohuwa yarinya* ๐Ÿ‘—๐Ÿ‘˜๐Ÿ’ƒ






Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ›
[4/13, 9:58 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................51



® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_ ๐Ÿ“



Bayan angama Had'a mata d'inkunan jabeer tayima waya akan yazo ya d'auketa, 'kofar gidansu ya sauketa sannan yaja motarsa yayi gaba da tsan-tsan kiyayyarta a cikin zuciyarsa, 

Washe gari ya rage saura kwana tara d'aurin auren zuby da jabeer, 
Zaune yake d'akinsa yahad'a uban tagumi hannu bibbiyu ba abinda yake tunani sai yanda ze zauna da Zuby amatsayin matarshi, ko kad'an bayajin sonta acikin zuciyarsa dai-dai da kwayar zarra, dan dai mamanshi kawai data nuna tsananin son auren shiyasa ya amince, besan me zuby tarika gayamataba kokuma takemata harta yarda da ita d'ari bisa d'ari kuma ta matsamashi akan sai ya aureta.

Wani guntun tsaki yaja gami da gyara zamanshi yajawo remote ya kunna TV lokacin ana labaran 'karfe takwas  

*Da farko ga kanun labaran, ayau ne shugaba muhammadu buhari ya sauka gida Nigeria daga tafiyar da yayi zuwa 'kasar England, Gobene Al'kalin babbar kotun jihar katsina ze gabatar da shari'a tsakanin wata matashiya me suna Hassana  Mansir Company inda take 'karar 'kawar 'yar'uwarta Zubaida wacce akafi kira da Zuby akan tana Zarginta akan kisan  'yar'uwa*.

A firgice jabeer ya mi'ke tsaye, yana mai-maita kalmar "Zuby takashe Hussaina, innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, komawa yayi ya zauna hankalinsa a matu'kar tashe, 
"Wannan bala'i dame yayi Kama? Anya zuby zata iya aikata kisan kai, meyasa Hassana takai zuby 'kara akan abinda batada kwakwkwarar sheda akansa, amma ita tasani Allah kaimu goben masu iya magana sunce duk wanda yace ze had'iye gatari sai asakar masa 'kota.




Da dare bayan daddy yadawo daga gurin aiki, bayan yasamu labarin shigar da 'karar da Hassana tayi, saboda duk illahirin garin ya d'auka Kowa Allah Allah yake gobe tayi suje kallo.

Momy yasamu zaune a falo ta buga uban tagumi, bayan tayimashi sannu da zuwa yake tambayarta "ina Hassana? "Tana d'akinta, momy tabashi amsa a ta'kaice, "kiramin ita, "to kawai tace ta mi'ke tanufi d'akin Hassana, Zaune ta isketa kan abin sallah da Qur'an a hannunta tana karantawa, domin samun nasara akan shari'ar daza'ayi gobe.

Da sallama Momy tashigo, bayan ta zauna gefen gado ta kalli Hassana "kizo daddynki na kiranki, "to ta amsa sannan tarufe Qur'an lokacin Momy ta dade da baro d'akin, a falo suka zauna itada Daddy suna jiran fitowar Hassana, daddy ya kalli Momy "anya yarinyar nan tana cikin Hayyacinta kuwa? "Saboda me kafad'i haka Alhj, saboda yanda ta shigar da 'kara kotu gashi har ana shirin zama na farko gobe batare data nemi shawarar yin hakan ba,

Murmushi Momy tayi "ai Alhj aikin gama yagama,tunda taji zata iya sai mu barta mugani.
Fitowar Hassanace ta katse masu maganar dasukeyi, cikin ladabi tasamu guri ta zauna, sannan tayima Daddy sannu da zuwa.

Suduka shiru sukayi na tsawon minti biyu kafin daddy yafara magana, "Hassana munji abinda kika aikata, amma amatsayinmu na iyayenki yakamata ki shawarcemu kafin ki yanke shawarar, ita shari'a da kike gani sa6anin hankali ce, kuma idan baka iya kama 6arawoba sai 6arawo yakamaka.

'Dagowa tayi ta kalli iyayen nata da fuskarta wacce Hawaye suka gama wankewa tace "dan Allah daddy da Momy ku gafarceni akan rashin shawartarku danayi, yanzu ba abinda nake bu'kata agareku sai addu'a inashaAllah naji ajikina nice da nasara, "To Allah ya bada sa'a "Ameen, ta amsa sannan ta kalli daddy, kuma dan Allah daddy ina Neman wata Alfarma agareku, "muna jinki daddy yafad'a, "inaso duk zaman daza'ayi a kotu yazama tare zamu tafi daku.
"InahaAllah zamuje Hassana kada ki damu kedai kije kiyita addu'a.

Nagode daddy, sannan ta kalli momynta Momy nagode, kuma inaso kuma ku tayani da addu'a.



Zuby kuwa tana zaune gidansu itada 'kawayenta tana nunamasu d'inkunan data amso daga gurin d'inki, tana gayamasu ranar dazatasa kowane kaya, 'kawayen nata kuwa ba abinda suke sai zuzutata suna yaba duk wani abu data fad'amasu ta tsara...

Ba zato ba tsammani kawai sai ganin yansanda sukayi gabansu, kusan su takwas mata hud'u maza hud'u,
Zumbur zuby tami'ke tsaye dan ba 'karamin razana tayiba kad'an yarage tasaki fitsarin wando.

'Daya daga cikin yansandan tace "zuby ko, munzo mutafi dakeU office d'inmu zaki amsa wasu tambayoyi.

Zuby ido ya raina fata zata fara masu gardama suka hankad'a 'keyarta tanaji tana gani aka sata a mota 'kawayenta kuwa duk sun fito sunyi cirko cirko, hakan yaba sauran yan unguwa damar tsayawa suma suna kallo, haka akaja motar zuby kuwa ba abinda take sai raba idanu.








Love u all my Fan's ๐Ÿ‘„๐Ÿ‰
[4/15, 6:55 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................52





Jabir zaune yahad'a hannuwansa duka biyu ya tallafi kumatunsa da alama yayi nisa cikin tunani, a zuciyarsa yana ganin gangancin Hassana da wannan mummunan hukuncin data yanke na maka zuby a kotu batare da tanada wata kwakkwarar shedaba.

 mama ce tashigo hannunta d'auke da kula da plate ta ajiye gabansa sannan takoma ta bud'e d'an 'karamin pridge d'inta ta d'auko ruwan pure water me sanyi guda biyu ta d'ora a plate takawo gabanshi ta ajiye, zama tayi d'an nesa dashi tare da zuba mashi idanu wani irin tausayinshi ya tsirga mata, tana matu'kar tausayama d'an nata shikuma haka Allah ya jarabeshi da rashin dacen mace tagari wacce duk wata harkallar da'ake ciki yanzu Itace sila, kuma gashi bata duniyar ma baki d'aya.

Wata nannauyan ajiyar zuciya tayi sannan takira sunanshi "jabeer... Firgigi yayi ya kalleta kamar Wanda yafarka daga bacci, sannan ya amsa "na'am mama.
"Tunanin me kakeyi haka? Ajiyar zuciya yayi sannan ya maida dubansa ga mahaifiyar tasa "mama Dole inyi tunani abubuwa da dama sun d'auremin kai nayi tunani nayi nazari amma ban hango wata kwakkwarar hujja da Hassana zata kai zuby 'kara ba.

Shiru yad'an ratsa na kimanin mintuna biyu sannan mama ta sauke ajiyar zuciya "to Jabir yazamuyi da wannan Al'amari tunda sunriga sunyi 'kara ai bakin al'kalami ya bushe mudai fatanmu Allah toni asirin koma waye ya aikata wannan mummunan aiki.
"Ameen jabeer ya amsa yana matukar jin ciwon abinda yafaru dashi arayuwa, sannan yajawo kular abinci yafara zubawa dan rabonsa da cin abincin kirki tun lokacin daya gane Hassana ba ita bace ainafin matarsa Hussaina.

Haka yafara cin abincin kamar yana cin magani badan yanajin dad'insaba Haka mama tatasashi gaba tana rarrashinsa har yad'anci da dama sannan yakora da ruwa me sanyi. 


**                **               **



A 6angaren Zuby kuwa tun anar da police suka angiza "keyarta Zuwa office d'insu suka shiga tuhumarta da tambayoyi amma fir ta 'ke'kashe 'kasa tace ita batasan kome game da kisan Hussaina ba. Haka yan sandan sukayi ta fama har suka gaji suka tattara kome suka ajiye suna jiran ranar daza'a fara gudanar da shari'ar a kotu.


*kotu* ๐Ÿ”จ

'Katon d'akin gudanar da shari'a yacika ma'kil da jama'a maza da mata yan kallo dakuma  wad'anda shari'ar ta shafa. Zuby kuwa tana tsaye Inda ake ajiye wad'anda ake zargi a kotu, sai raba idanu takeyi, gefe ga d'ansandan dake tsare da ita,
yan kwanakin datayi a kulle har fatar jikinta tayi duhu sai 'kuraje dasuka firfito a jikinta wad'anda suke nuna alamun tasha cizon sauro ga wata irin rama datayi


Guri d'aya kuma momy ce zaune Sai Hassana gefenta wacce tunda tashigo d'akin shari'ar take faman karanto duk wata addu'a datazo bakinta dan neman nasara gurin ubangiji.

Daddy shima suna zaune a kujerar gaba yayinda Jabir yake kujerar dake bayanshi,
Kotu tagama cika mutane an kaure da surutu kowa na fad'in albarkacin bakinsa, shigowar Al'kali yasa mutanen gurin yin shiru tare da mi'kewa, haka Al'kalin ya isa mazauninsa ya zauna sannan sauran jama'a suka zauna, wani littafi dake gaban Al'kalin ya bud'e yayi wasu yan rubuce-rubuce sannan yayi gyara murya yace "afara gabatar da 'kara ta farko.

Me gabatarwa ya mike tare da wata takarda a hannunsa yafara karantawa kamar haka "shari'armu ta farko shine wacce Hassana mansir company take 'karar 'kawar yayarta Zubaida wacce akafi sani da zuby akan tana zarginta da kisan gillar da akayima 'yar uwarta kuma abiyar Haihuwarta wato Hussaina mansir company, bayan yagama karantawa yakoma ya zauna.

Al'kali ya kalli Zuby yace kece Zubaida? Zuby ta gyad'a kai kamar 'kadangarwa tace "Eh nice ya mai girma mai shari'a, Alkali yace kokinada lauya Wanda ze iya kareki tace "inadashi, nanma Al'kali yayi "yan rubuce-rubucensa sannan yace ina lauyan wanda ke 'kara da kuma lauyan wacce ake 'kara.

Lauyan Zuby ne yafara mikewa yafara gabatar da kanshi sannan lauyan Hassana shima yagabatar da kanshi.






*Kuyi ha'kuri kufara da wannan inshaAllah kafin kome ya dai-daita, kuma inaso zanyi amfani da wannan dama inmi'ka dumbin godiyata ga masoyana a duk inda suke nagode da kulawar da kuka nuna agareni najina da kukayi kwana biyu shiru kuna ko'karin kirana dan jin lafiyata, banida bakin dazan godemaku sai dai ince Allah saka da Alkhairi ya'kara dan'kon zumunci*
[4/17, 8:55 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................53




Al'kali ya gama yan runbuce-rubucensa sannan yafara magana "ko lauyan wacce ake 'kara yanada abin cewa.

Lauyan zuby ya mike "inada magana ya mai girma mai shari'a, da farko inaso in tabbatarma wannan kotu me Adalci zuby ba ita bace ta kashe Hussaina, kodan Idan akayi la'akari da 'kawancen dake tsakaninsu dakuma aminci da yarda da juna, bayan wannan an tabbatar da marigayiya Hussaina batada wata 'kawa bayan zuby, kuma Kowa yasan zuby yasan kyawawan halayenta bazata iya koda kashe 6era ba, barantana mutum, kuma 'kawarta aminiyarta, saboda yarda da ita dakuma kyawawan halayenta yasanyama mijin ita marigayiyar yayi kwad'ayin aurenta Wanda a halin da ake ana saura kwana goma a daura aurenta ita Hassana tayi 'kararta akan  tana zarginta da kisan yar'uwarta wacce batada wasu kwararan shedu,........ Yana kaiwa nan ya russuna yace "nagode ya mai girma me shari'a, sannan yakoma ya zauna.

Bayan Al'kali yayi rubutu, sannan yad'ago yace "ko lauyan wacce ke kara yanada abin cewa, sai lokacin lauyan Hassana yami'ke ya'kara gabatar da kanshi sannan yafara magana.
"Ya mai girma mai shari'a inaso inyima wacce ke 'kara wasu yan tambayoyi, Alkali yace "anbaka dama, "kotu na bu'katar ganin Hassana a gabanta, wani mummunan fad'uwar gaba Hassana taji sannan tami'ke tana karanto addu'oin samun nasara abakinta.

Bayan tatsaya inda aka umarceta lokacin lauya yafara jera mata tambayoyi tana bashi amsa, karshe yace Hassana to ko zaki iya bayyanama kotu dalilin dayasa kike zargin zuby akan kisan 'yar'uwarki? Hassana tagyara tsayuwa tace "itace tasameni har gida tafad'amun lokacin ina zaune gidan jabeer amatsayin matatarsa marigayiya Hussaina, kuma sannan ta gargadeni akan in gaggauta barin gidan da ita yadace da ta zauna amatsayin matar gidan sannan kuma tayimani kashedi da idan na kuskura nafad'ama wani nima zata kasheni.

Lauya ya'kara jefarta da wata tambayar "taya akayi kika zauna gidan jabeer amatsayin matarsa alhalin kuma yana auren 'yar'uwarki?

Wani irin kuka ya kwacemata dan tunowa datayi da abinda yafaru da ita na *AUREN TAGWAYE* dasukayi itada yar'uwarta, ahankali tasa hannu tashare hawayenta sannan takwashe labarin abinda yafaru kaf tsakaninta da marigayiya Hussaina tundaga had'uwarsu da Hafiz har zuwa lokacin da taro'keta akan tanaso ta zauna gidanta amatsayin ita akan cewa zataje bikin 'kawarta Wanda zubyn ce takitsa mata haka kuma tayi sa'a Hussainar ta amince shine tayi amfani da wannan damar takasheta dan tasamu damar aure mijinta, wannan shine iyakar abinda nasani.

Lauyan ya kalli al'kali wanda yake rubutu acikin littafinsa yace "inaso kotu tabani dama inyi wasu 'yan tambayoyi ga mijin marigayiyar, alkali yace "anbaka dama.

Haka kotu ta umarci ganin jabeer, shima bayan yan tambayoyi da'akayimasa yaba kotu labarin iya abinda yasani tundaga aurensa da Hussaina dakuma zaman da Hassana tayi agidansa amatsayin ita marigayiya Hussainar. Daga kan tambayoyin da lauyan yayima Jabeer yajuya gurin Al'kali yace nagode ya mai girma mai shari'a, sannan yakoma ya zauna.


 Lauyan Zuby yami'ke yana gyara rigarsa, yace "ya mai girma mai shari'a labarin da wacce ke 'kara ta bayar kwata-kwata beda nasaba da abinda ake 'kara Kanshi, saboda haka ina ro'kon wannan kotu mai Adalci datayi watsi da wannan shari'ar kuma sannan abima zuby hakkinta akan 'kazafin kisa da aka li'kamata wanda batajiba bata ganiba.

Al'kali yace "ko lauyan wacce ke 'kara yanada wasu 'karin bayani? Lauyan Hassana yami'ke yace "babu yamai girma mai shari'a, bayan Al'kali yayi yan rubuce-rubucensa sannan yadago ya kalli Al'ummar dake cike ma'kil cikin wannan kotu yafara jawabi 


"Abisa shedu dakuma bayanai da lauyoyi suka gabatar agaban kotu, kotu ta gamsu da bayanan kowane 6angare dakuma shedun dasuka gabatar saboda haka kotu tayi watsi da wannan shari'ar saboda batada makama, sannan kotu taba zuby damar d'auka 'kara akan 'kazafin kisa da aka li'ka mata.

Wani irin kukan takaici Hassana tafashe dashi dan jin abinda al'kali yafad'a, Zuby kuwa wani shu'umin murmushi tayi, take kotu ta kaure da surutun jama'a Kowa na fad'in albarkacin bakinsa.

Al'kali yabuga teburin dake gabansa sannan kotu tayi tsit, yana shirin cigaba da jawabi kawai sai ganin wani matashin saurayi sukayi yashigo kotun yana cewa "nine sheda na 'karshe wanda zan war-warema kotu kome da kome akan wannan case din.

Nanfa kallo yakoma kan wannan matashin sunayin ido hud'u da zuby gabanta yayi wani mummunan fad'uwa, Jikinta yafara kyarma wata irin zufa ta keto mata, Hassana kuwa kallonsa takeyi tanaso ta tuna inda tata6a ganin wannan fuskar amma takasa tunowa.






Love u all my Fan's.
[4/19, 1:45 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................54





Baki d'ayan hankalin mutanen dake cikin kotun yakoma kan wannan saurayin daya shigo yana fadin zebada sheda, Hassana kuwa mamakine yakamata azuciyarta tace " toshikuma waye wannan ? meya sani game da mutuwar 'yar'uwata,? anya akwai wata sheda daxe bada wacce zatasa Al'kalinnan ya saurareshi tunda har abinda nafad'a besa ya yarda cewa zuby takashe Hussainaba.


Muryar Al'kalince tadawo da ita daga tunanin datake, jitayi yana fad'in "saurayi daga ina? Kotu tanaso tasan ko kai waye kafin kabada sheda agabanta.

'Kara dai-daita nutsuwarsa yayi sannan yafara magana "sunana *Hafiz* kuma ni saurayin Marigayiya Hussaina ne, wannan kuma friend d'inace yafad'a yana nuna Zuby.
Amma ita sona take kuma batada burin daya wuce in aureta, nikuma a lokacin bata gabana saboda ko d'an iska yanaso ya auri mace tagari ba irin zuby ba wacce tagama watsewa a titi, kwatsam saita fahimci muna soyayya da 'kawarta marigagyiya Hussaina, muna cikin wannan halin mahaifin Hussaina yayimata aure saboda ganin ta 6ullo da wasu Halaye marassa kyau.

Haka dai yacigaba dabada labarin iyakar abinda yasani dangane da mutuwar Husssaina  kuma ya tabbatarma kotu zuby itace takashe Hussaina saboda tanason ta auri mijinta dan ganin cikin irin jin dadin datake dakuma yanda mijinta ke Sonta.

A lokacin nikuma nabukaci da muhad'a kai idan ta auri jabeer ta kasheshi ta kwashe dukiyarsa tadawo muyi aure dan inada tabbacin babu wani namiji datakeso sama dani, jabir najin haka besan sanda yakalli zuby ba yana jin wata muguwar tsanarta cikin zuviyarsa, dama tun can ba sonta yakeba.

Hafiz yacigaba da magana shine tanuna rashin amincewarta, nikuma alokacin na kunna mata recording din danayimata lokacin datake jaddadamin ita takashe Hussaina, nan take ta tsorata dajin wannan recording dan nayimata barazanar muddin bata amince da bu'katataba zan dam'ka wannan recording hannun hukuma, shine tacemin inbata kwana biyu zatayi shawara.

Ranar data nemeni dan gayamin shawarar data yanke ranar tazubamin guba a lemu dan kada natonamata asiri, Allah yasa inada sauran numfashi 'kanwata takaini asibiti da taimakon lokitoci nasamu kaina, shine nasa 'kanwata tabugama Zuby waya tafad'a mata cewa namutu, tunda aka sallameni daga asibiti na tattara kayana nakoma garin Kaduna gurin abokina, ina can nasamu labarin wannan shari'a shine nazo dan inbada sheda yanzu hakama saukata garin kenan nawuto nan.

Yana kaiwa nan yayi shiru, mutane suka fara kallon kallo ana magana 'kasa-'kasa Kowa nafad'in albarkacin bakinsa, Hassana kuwa mamakine yagama rufeta, haka Momy da daddy, Zuby kau raba idanu kawai takeyi  duk illahirin jikinta kyarma yakeyi, zufa tagama rufeta kamar wacce aka she'kama ruwa.



Bayan surutun yad'an lafa Al'kali kuma yayi 'yan rubuce-rubucensa yad'ago ya kalli Hafiz yace "Hafiz kozaka iya gabatarma kotu da wannan recording din dakace ka d'auka lokacinda Zuby take jaddadama itace takashe Hussaina, Hafiz yace Eh ranka shi dad'e yasa Hannu aljihu yaciro wayarsa ya kunno inda recording d'in yake wani mutumi dake zaune gaban Al'kalin ya amshi Al'kali yabashi dama sannan ya kunna mutane sunyi tsit ana saurare bako shakka muryar zuby ce  lokacin datake cewa _of course bazan tsaya ina jayayya dakaiba nina kashe Hussaina saboda tashiga gonata_  mutane najin Haka suka d'au salati wasu suka fara Allah wadai da halin Zuby.

Saida Al'kali yabuga teburin dake gabansa sannan kotun ta saurara,  "Abisa shedun da kotu tasamu tagamsu da cewa Zuby itace takashe 'kawarta Hussaina dan tanaso ta auri mijinta, saboda Haka wannan kotu me Adalci ta yankema Zuby hukuncin kisa ta Hanyar rataya, muna fata wannan zezama Izna gamasu Hali irinna zuby.

Wani irin murmushin farinciki ya subuce daga bakin Hassana tafad'a Jikin momynta tana kukan farin ciki.

Zuby kuwa wata mahaukaciyar 'kara tasaki tana kuka tana tsinema Al'kalin wai beyi hukuncin tsakani da Allah ba

Haka kotu ta watse zuby na hauka tana zage zage da fizge-fizge aka angiza 'keyarta cikin ba'kar mota wacce ake saka masu ba'kin hali irinnata.






Love u all my Fan's
[4/23, 6:35 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................55




      *Bayan Wta Daya*
Jabir ne zaune a office dinsa tunani barkatai acikin zuciyarsa, a wani 6angaren kuma na zuciyarsa soda 'kaunar Hassana ne ke d'awainiya dashi, tunanin irin zaman dasukayi yakeyi, Lallai Hassana macece waccce kowane namiji zeyi fatan tazama mallakinsa, kuma uwar yayansa.

 yarasa wace hanya zebi ya bayyana mata irin tsananin sondayake mata, jiyayi zaman office din ba dad'i saboda haka tattara takardun dake gabansa yayi ya ajiyesu tare da rufe office din, kai tsaye inda ya ajiye motarsa yanufa yabud'e yashiga sannan yasa key yatayar da motar yad'au hanyar gida, zuciyarsa cunkushe da tunane-tunane.


'Kofar gida ya ajiye motarsa, sannan yafito, da nusaiba suka had'u cikin fara'a da sakin fuska take gaisheshi, "yaya jabeer sannu da Zuwa, "yauwa ya amsa sannan ya tambayeta ina zaki haka? Cikin ladabi tabashi amsa "nan 'Kasan layinmu zanje gidan kitso, "owk to adawo lafiya, yafad'a tare da wucewa kai tsaye cikin gidannasu, da sallama yashiga, mama ya iske zaune tana sauraren redio, jin sallamarsa yasa tarage sautin redion tare da amsa sallamar "kaine yanzu da rana nan, tafad'a tana kai dubanta gareshi, lokacinne kuma ta fuskanci akwai damuwa tattare dashi, bissmillah zauna tafad'a tana tura mai kujerar dake kusa da ita.

Fridge yanufa yafara d'auko ruwa me sanyi sannan yadawo ya zauna tare da sauke wata ajiyar zuciya, ruwan yafasa yafara sha, ahankali yaji wani sanyi na sauka a zuciyarsa, saida yakarasa shanye ruwan sannan ya kalli mama ya gaisheta cikin girmamawa, bayan ta amsa, shiru yad'an ratsa na kimanin minti biyu, sannan mama ta numfasa tace "da alama akwai damuwa tattare dakai, shin miye damuwarka kafad'amin amatsayina na mahaifiyarka idan inada maganinta zanyima idan kuma babu inbaka shawara, idan itama bazatayiba zan taimakama da addu'a domin babu abinda ya gagari Allah.

Hakane mama, ba wata damuwa bace tafe dani, inasone Hassana ta maye gurbin 'yar'uwarta amma kwata-kwata nakasa tunkarar mahaifinta da maganar.

Murmushi mama tayi me d'auke dajin dad'i tace "ni kaina na jima inayima kwad'ayin auren Hassana yarinya me hankali da ladabi da biyayya, ga girmama nagaba da ita, abinda yasa banyima maganaba Dan ina tsoron kada kabi za6ina kuma a maimaita yar gidan jiya, watakila bakada ra'ayin hakan, amma yanzu tunda ka furta da bakinka kabar kome a hanuna inshaAllah kome zezo da sau'ki.
"Kamar da yaushe Alhj yake gida zanje ni insameshi, 
"eh to yana komawa gurin 'karfe biyu na rana sai yakuma fita 'karfe hudu na yamma.
"Kada kadamu inshaAllah gobe zanje gidan dakaina, 

Cike dajin dad'i jabeer yayima mamanshi godiya, haka suka d'an ta6a fira, saida yaci abinci sai bayan azahar yabar gidan, zuciyarsa cike dajin dad'i dan abinda mama tafad'a mai gani yake kamar yasamu Hassana yagama.


A 6angaren Hassana kuwa tun ranarda aka yankema Zuby hukunci a kotu take jinta cikin wani farinciki, dan jitake kamar da hannunta tad'au fansar kisan da'akayima 'yar'uwarta.
Wani 6angaren kuma na zuciyarta tsananin son jabeer da 'kaunarsa ke d'awainiya da ita, dan d'an zaman dasukayi da jabeer ta fuskanci halayensa akwaishi da tsananin ha'kuri, ga yawan ibada, wasu hawaye taji sun zubo mata Wanda ita kanta batasan dalilin fitarsuba, tasa hannu tagoge sannan tad'aga hannuwanta sama tafara rokon Allah, 
"ya Allah ka mallakamin jabeer amatsayin mijina, yazamo uban yayana, Allah ameen tafad'a tare da saukar wasu sabbin hawaye a kumatunta.

Kusan kullum haka take fama da dawainiya da soyayyar jabeer acikin zuciyarta tarasa Wanda zata fad'amawa kota d'an samu sauki dan ita dama bata cika kwashe-kwashen kawayeba, sai kuma ga abinda yafaru da 'yar'uwarta ta sanadin 'kawa tarasa rayuwarta, itakam ta tsani 'kawa duk yanda take.





*ina Baku ha'kuri na rashin samun typing akai-akai, kunsan jiki da jini, akace yauda gobe sai Allah*


Love u all my Fan's๐Ÿ“
[4/23, 7:26 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................56




Washe Gari Hassana ce keta kai kawo tsakanin falo da kitchen, kallo d'aya zakayimata ka tabbatar tana cikin nishad'i haka kawai yau ta tsinci kanta da jin wani matsanancin farinciki, yanzuma girki tagama shine take jerawa kan dining, bayan tagama takoma tagyara kitchen ta goge sannan tawuce d'akinta kai tsaye toilet tashiga tashe'ka wanka, sannan ta d'auro Al'wala dan ganin lokacin sallar azahar yayi, tana fitowa ta zura wata doguwar riga tare da saka hijab ta shimfid'a abin sallah, saida ta kammala sallar tayi addu'o'inta tashafa sannan ta isa gaban dressing mirror tafara shafa wani cream me dadin 'kamshi sannan ta murza powder a fuskarta tashafa kwalli tashafama lebenta man le6e.

Wadrope tanufa kai tsaye ta d'auko wasu riga da siket na material orange colour d'inkin yayi matu'kar kyau bakamar datasaka ajikinkta, sai jikin nata tare da Hasken fatar jikinta ya'kara fiddo da kyan material d'in.


Kitchen tanufa tazubo abinci tare da d'auko robar ruwa me sanyi, da madarar holandia takoma d'akinta tafaraci zuciyarta wasai kamar wacce akayima albishir da gidan Aljanna, bayan ta kammala cin abincin ta d'auki plate ta maida kitchen tana mamakin kanta yanda yau taci abinci me yawa haka kamar ba itaba, wanda rabon dataci abincin kirki tun ranar data zauna gidan jabeer amatsayin 'yar'uwarta sai kau yau, a zuciyarta tace anya ba wani abu ke shirin faruwa daniba......



Tana cikin wannan tunanin taji tsayuwar motar daddy, tananan hartaji shigowarsa falo sannan tafito tayimashi sannu da zuwa tawuce d'akinta, binta yayi da kallo da alama akwai abinda yake tunani dangane da ita.

Momy kanta ta lura da hakan, itace tadawo dashi daga tunanin dayake ta hanyar 'kar6ar jakar hannunsa tawuce d'akinsa, shikuma yabi bayanta,  ruwan wanka tafara had'a mashi saida yayi wanka ya canja kaya zuwa masu sakai-sakai sannan suka fito zuwa dining, Momy da kanta tazuba masu sannan suka fara ci.

Bayan sun kammala cin abincinne Momy ta kwalama Hassana kira, da sauri tazo tace "gani momy.
Momy ta umarceta data kwashe kayan dasukaci abinci, "to ta amsa sannan tafara kwasa tana kaiwa kitchen saida ta kammala ta gyara gurin tsaf, sannan takoma d'aki wayarta ta jawo ta kunna data best group dinta tashiga na *Ciwon ya mace* ta iske su *Mmn Ummi da Mmn zee da Momyn ramadan da Ameena PA* da dai sauransu anata raha itadai mutanen grouf din na matu'kar burgeta, sallama tayimasu suka amsa, nan fa Ameenoo tafara "oyoyo ga 'kawata, nan Hadiza tace kaji shishshigi 'kawarki ko tawa, murmushi Hassana tayi tace "Hmm kudakata aini banida 'kawa duk grouf dinnan kowama 'kawatace dan gaskiya kuna matu'kar burgeni kun iya zama da mutane.

A falo kuma momy ta kalli daddy Wanda ya maida hankalinsa kan jaridar dake hannunsa, tace "waini Alhj haka zamu zubama yarinyar nan ido tayita zama agida, kuma ita gashi tunda canma bata kula kowa barantana yanzu.

Shiru daddy yayi na kimanin mintuna biyar, itakuma Momy ta zubamai idanu tana jiran taji me zai fad'a.

Numfasawa yayi sannan yace "to me kike tunanin zanyimata kuma,?
 Momy tad'an gyara zamanta "nida cewa nayi mezai hana tacigaba da karatunta kafin kuma muga abinda Allah zeyi.


Wani mugun kallo daddy ya watsama Momy wanda saida yasa hantar cikinta ta kad'a sannan yafara magana cikin d'aure fuska
 "kada ki kuskura in 'karajin wannan maganar daga bakinki, koda zatakai shekara nawa a gidannan babu maganar cigaba da karatu, munanan tare da ita har lokacin dazataga dama tagfito da miji tayi aure.

Yana gama fad'in haka ya kwashe jaridarsa yawuce d'akinsa yabar Momy zaune sake da baki.






Love u all my Fan's ๐Ÿ“
[4/24, 6:32 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................57




Momy kuwa tunda daddy yagama magana yashige d'akinsa yabarta zaune a falo, tunani barkatai takeyi a zuciyarta tana ganin kamar shawarar data kawoma daddy batada makusa amma sai gashi yanda ya nuna kwata-kwata bazebi shawarar tataba.

Tayi zurfi cikin tunani taji kamar ana sallama a bakin 'kofar falon 'kara saurarawa tayi jitayi ankara doka sallamar mi'kewa tayi tare da amsa sallamar ganin maman jabir datayi yasa tasaki murmushi "a'a yau kune a gidannamu lale maraba sannu da zuwa, "yauwa tafad'a itama fuskarta d'auke da murmushi.

Bayan sun gaisa momy tacika gabanta da kayan sanyi, mama tazuba lemun tasha sannan ta ajiye cup ta maida dubanta ga momy "Allah sa dai Alhj yana gida dan maganace me matu'kar muhimmaci take tafe dani.

Numfasawa momy tayi kafin tace "eh yananan bari namaki magana dashi, sannan tanufi d'akin daddy kwance ta iskeshi ya kalli bangon d'akin da alama yayi zurfi cikin tunani, zama tayi bakin gadon sannan tasanar dashi zuwan maman jabeer,

Tare suka fito Alhj na gaba momy na bayanshi, zama sukayi baki d'ayansu a falon bayan daddy sun gaisa da maman jabeer nan take sanar dashi maganar dake tafe da ita na nemawa jabir auren Hassana, da kuma yanda jabeer din yasanar da ita jiya.

Murmushi Daddy yayi wanda ya nuna alamun farin ciki tattare dashi sannan ya numfasa yace "in banda abin jabeer aini matsayin d'a na d'aukeshi koshi da kanshi yafad'amun ai bazan hanashi jininaba inshaAllah babu wata damuwa, yanzu abinda yakamata shine yafara zuwa su fuskanci juna shida yarinyar,


Godiya maman jabeer tashigayi, tana yaba halin kirki da dattako irinna Alhj mansir, mutumne me tarin dukiya, amma Allah be d'oramashi girman kaiba, da raina talaka.
Haka sukayi bankwana momy tayimata rakiya har harabar gidan suna 'kara tattauna al'amarin yaran, da alama ita kanta momy taji dad'in hakan dan kowane iyaye zasuyi burin 'yarsu tasamu nagartaccen namiji kamar jabeer, mutum me ilimi da ri'ko da addini, ga kuma ri'kon amana.


**                **              **

Sanye suke cikin kayan uniform kalar dark blue, matane zallah zaune suke cikin wani 'kazamin d'aki dan ba abinda ke tashi d'akin sai wani irin matsanancin wari, can na hango wata matashiyar yarinya zaune tahad'e kai da gwiwa da alama kuka take, itama sanye take da kalar uniform d'in jikin rigarta ansa number itace number ta sha takwas,  wata 'katuwar mata nagani taje kanta ta tsaya ta ta6ota tana fad'in "yaya dai 'yanmata?
Ahankali wacce akayima maganar tad'ago ta kalli wannan wannan 'katuwar matar, fuskarta sharkaf da hawaye tayi wani ba'kikkirin duk ta rame, jin wannan 'katuwar matar takira sunanta "Zuby yadai yanaganki haka, zuby tasa hannu ta goge hawayen dake idanunta ta 'kara gyara zama batada niyyar yin magana.

Wannan 'katuwar matar dake tsaye ta gagga6e da wata mahaukaciyr dariya cikin muryarta wacce tafi kama data 'kato, saida tayi dariya me isarta sannan tadafa kafad'ar zuby tace "Haba zuby ke kullum kuka kamar ke kad'aice kiduba kiga fad'in wurinana kowa harkar gabansa yake amma ke kinsama ranki tunani kin'ki ci kin'ki sha duk kin lalace.

Kallo zuby tabi mutanen gurin dashi kowace kuwa harkar gabanshi yakeyi kamar ba gidan yari sukeba, sannan tamaida dubanta ga matar tace dole inyi kuka dole ci da sha ya gagareni, rai raifa nakashe, dole tun duniya inga sakayya ko zaman gidannan ma kad'ai bala'i ne.

Wata mahaukaciyar dariya matar tasake bushewa da ita "tace lallai yarinyar nan rayuwarki na 'Kazan ruwa, kowa tuba dan wuya ba lada, ni yanzu jiran lokacin daza'a sallameni kawai nake ind'ora daga inda natsaya.







Love u all my Fan's ๐Ÿ‡
[4/25, 8:13 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................58





Kallo kawai zuby tabita dashi dan tasan duk abinda tafad'a haka yake *Har a zuciya* na (Fiddausi so Dangi) amma itakam ayanzu tayi nadamar abinda ta aikata, gashi yanzu son abin duniya yakaita ya baro.

Suna cikin wannan maganar wannan katuwar matar taji an d'auketa da wani migun mari, waigawa sukayi bakin d'ayansu wata azzalimar 'yar sanda ce suka gani, dan Duk illahirinsu masifar tsoronta sukeyi har suna suka sakamata inspector zalima, ai da gudun tsiya wannan 'katuwar matar tabar gurin duk kuwa da uwar 'kibar dake jikinta.

Zuby kuwa saboda rashin 'karfin jiki kasa motsawa tayi daga wajen, hakan yaba inspector zalima damar wankamata lafiyayyun mari har guda biyu, dan gani take zuby ta rainata kowa na gudu atafi aiki amma ita ta gagara tashi, zuby kuwa yunwa da kishi, da rashin karfin jiki yahanata mi'kewa ganin haka inspector Zalima tasa bulala tacigaba da zabgama Zuby, saida tayimata rud'u-rud'u duk tafasa mata jiki sannan tabarta. Kuma sannan tatasa keyarta zuwa aikin dazasuyi na kwasar bola da wankin toilet dinsu mai d'auke da 'kazantu kala-kala. _Niko zee kallon zuby kawai nake tsananin tausayinta kwance a fuskata, nace lallai Zuby yau duniya tamata gwatson mage_.


       *Bayan wata 2*

Shirye-shiryen biki ya kankama tsakanin 6angarori guda biyu, Maman jabeer hidima take sosai dan jin bikin take kamar shine tafarayi a rayuwa, kallo d'aya zakamata ka tabbatar da farinciki tattare da ita.

Momy kuwa dama wannan shine bikin dazatayi na farko dan lokacin bikin Hussaina ba'ayi wani shagaliba.

6angaren jabeer ango kuwa kullum cikin hidima yake dan yau saura sati bikin yariga yagama gayyatar duk wanda ze gayyata.

6angaren amarya kuwa wata 'kawar Momy ce ta d'auketa tatafi da ita gidanta can akeyimata gyaran jiki na amare, tsawon sati biyu ana abu guda tundaga kan dilka halawa, da sauran nau'ikan gyaran jiki, sai ingantaccen tsimi me kyau wanda ke gyara mace kullum tajita cikin ni'ima.

Ana saura kwana bakwai d'aurin aure Hassana tadawo gida, da niyyar saura kwana biyu bikin zata koma ayimata gyaran gashi da lalle, wani sihirtaccen 'kamshi ketashi daga Jikinta ga wani haske da santsi da fatarta ta'kara, dole ko mace ta kalleta takuma kallonta dan fuskarta har wani shek'i takeyi. Zaune take d'aki Momy tatasata gaba da wani tsimi da aka had'a na fruits tanaso ta shanye itakuma sai shatake tana 6ata fuska kamar zatayi amai, sotake Momy tabar d'akin ta ajiye.

Lokacin wayarta tayi ringing sunan Hubby tagani akan wayar, kasa d'agawa tayi tana kallon Momy.
Momy tace ki d'aga mana kinbar waya yana ringing, murmushi tayi sannan tace ina tunanin yazone dan munyi waya dashi yacemin gashinan zuwa yanzu.

Daure fuska Momy tayi minti goma nabaki kiyi ki dawo, ince nafad'amaki ya daina zuwa haka, idan kukayi ha'kuri sati d'aya yarage ami'ka mashi ke baki d'aya.

Cike dajin kunya Hassana ta d'auki wani madaidaicin hijab tasaka sannan tafita tsaye ta iskeshi jikin motarsa, batace yashigoba dan taji gargad'in Momy datace minti goma tabata, tana karasawa kusa dashi yaji wani sihirtaccen 'kamshi yadaki hancinsa, ahankali yadago idanunsa yakai dubansa gareta, yasalam yafad'a tare da sauke wata ajiyar zuciya.
Jiyake kamar ya rungumeta yahad'ata da jikinsa yacigaba da sha'kar daddad'an kamshinta

"Sannu da zuwa tafad'a cikin sassanyar muryarta, kanta sadde tana kallon kasa, "yauwa sannu dai amarya, yakike ya kuma hidima?

Murmushi tayi "Hmm hidima ai tana wurinku angwaye, "haka kike gani koh, amma ni a tinanina biki ai na amare ne.

Murmushi kawai tayi dan bataso firar tasu tayi tsayi, shiru yad'an ratsa na yan mintuna sannan jabeer yace "dama zuwa nayi inji dame-dame kk bu'kata na hidima dan naga idan nayi shiru ke bazakice komeba.

Eh ai bana bu'katar kome dan bawani bidi'a za'ayi a bikinnamuba walima kawai zamuyi, tonaji amma baki bu'katar kome na walimar?
"Eh bana bu'katar kome dan momy tagama had'a mana kome.
"Lallai Allah sakama Momy da Alkhairi amma dukda haka ga wannan kirike gurinki koda zaki bu'kata bandir d'in yan d'ari biyar yami'kamata sannan sukayi bankwana yawuce tana d'aga mashi hannu harya 'kule sannan takoma gida.






Love u all my Fan's ๐Ÿ‰
[4/27, 3:01 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................59





Yau yakama saura kwana biyu d'aurin auren Hassana da jabeer, yau ne kuma taje akayimata had'add'en gyaran gashi, tare da zana mata flower me kyau a hannunta, wani sihirtaccen kyau tayi dan idan ka kalleta sau d'aya dole ka kara.

Washe gari ana gobe d'aurin aure 'yan'uwa da abokan arziki da yan tsirarun 'kawayen Hassana sun taru a harabar gidan, domin walimar da wa'azi da aka shirya.

Da misalin 'karfe hud'u aka fara gabatar da wa'azin inda wata shahararriyar malama tayi nasiha kan zaman aure, amarya Hassana kuwa tasha kyau dan wata tsadaddiyar atamface Jikinta sai babban hijab data saka.

Da misalin 'karfe shidda aka kammala wa'azi aka rufe taro da addu'a tare dayima amarya da ango fatan zama lafiya da samun zuri'a tagari.

*Rana bata 'karya inji masu iya magana, sai dai uwar d'iya taji kunya*

Dandazon mutane manyan yan kasuwa da 'kusoshin gwamnati ne tan'kam 'kofar gidan Alhj mansir company, wad'anda suka halarci d'aurin auren Jabeer da Amaryarsa Hassana, wanda aka d'aura kan sadaki dubu hamsin.

Ansha shagalin biki taro yatashi lafiya, amarya ta tare gidanta mutane Kowa yanatasa Albarka.

**                 **              **

*Bayan Wata takwas*
 
Tunda tatashi take faman kuka kamar zata cire ranta, idanunta sun kumbura sunyi suntum sakamakon rashin baccin datake samu, kusan wata da watanni, kullum cikin damuwa take amma da alama damuwar tayau tafi ta kullum.

Wasu yansanda  kusan su hudune suka tsaya kanta, d'aya daga cikinsu ya kwatsa mata tsawa da alama Hausa bata zauna Mashi a bakiba, "oya les go, jiki a sanyaye *Zuby* ta taso tabisu a mota aka sakata, saida akayi tafiya me nisa sannan suka tsaya gaban wani 'katon get megedi yabud'e masu get suka shige, daga nan suka ajiye motar sannan sukayi tafiya me d'an nisa wacce tasadasu da wani d'aki Wanda anan suka iske wasu 'kattin ba'ka'ken mutane tsai-tsaye sunata mazurai wani dogon bencine sai wata igiya ta zuro anyi kullin 'zarge da ita dai-dai yanda kan mutum ze shiga.

Zuby na tsaye ta d'aga kai ta kalli gurin wasu zafafan hawaye suka sauko kan fuskarta, batayi 'ko'karin gogewaba haka suka ri'ka zuba wasu nabin wasu. Wata mace daga cikin yansandan aka mi'koma wata ba'kar hula me zurfi tasaka kan zuby ciki bayan and'orata kan wannan dogon tebur, sannan aka sa'kalo kanta cikin wannan igiyar, wani ba'kin d'ansandan fuskarsa bako annuri yasa 'kafa yature tebur d'in haka yaba igiyar damar tsuke wuyan zuby tayi sama da ita, saiga 'kafafunta suna lilo tanata harbe-harbe kafin daga nan rai yayi halinsa.
*Wannan shine 'karshen muguwa Zuby maci amana, kuma yar ta'adda*


Hafiz kuwa tun bayan da yabada sheda a kotu ya tattara yanashi-yanashi yakoma kaduna da zama, ya canja hali, yazama mutumin kirki kullum zaka sameshi yana istigifari, a haka Allah yahad'ashi da wata yarinya yar mutunci cikin 'kan'kanin lokaci suka sasanta bayan wata biyu aka d'aura masu aure, suna zaune a unguwar dosa Kaduna.


 **                **             **

Ahankali take takawa saboda nauyin da cikinta yayimata, cikin wata shidda amma idan ka kalleta yanayin Girman cikin saika d'auka yayi wata tara,ga kumburi tana fama dashi,
 kitchen tanufa dan sama masu abinda zasuci na rana.

Lokacin jabeer yayi horn megadi yabude masa get, gurin ajiye motoci yayi parking sannan yashigo gidan da sallama, shiru yaji kuma be ganta a faloba bedroom yanufa nanma bata nan, can yajiyo motsinta kitchen can yanufa isketa yayi tanata ha'kilon had'a musu jalouf din kus-kus harma ta kammala tana shirin d'aukowa takai kan dining, da sauri ya amshi kular hannunta, ya ajiye  sannan ya rungomota jikinsa bayanta had'u da 'kirjinsa sannan ya d'ora hannunsa kan 'katon cikinta yana shafawa ahankali, "haba my sweet nafad'a maki baniso kina wahalar da kanki kina wahalarmin da baby, bari kigani, hannu yasa ya d'auki kular abincin yakai kan dinning table yadawo ta mi'ko mai plate yakai sannan yadawo tami'kamashi cup din fruit salad d'in data had'a yaji 'kan'kara sai ra6a jikin jug din

Bayan sun kammala wannan da kanshi yahad'a mata ruwan wanka sannan yarakata har toilet, yana zaune harta gama wanka da kanshi yashafamata lotion me sanyi sannan ya d'uko mata wata doguwar riga me saukin nauyi ta sanya.
Kama hannunta yayi ya zaunar da ita bakin gado "ina zuwa bani minti goma yafad'a toilet yashiga yashe'ka wanka yafito ya murza lotion sannan yasaka wasu 'kananan kaya riga ash marar hannu sai bakin wando three quarter, sannan yakama hannunta suna takawa ahankali kamar makaho da d'an jagora har kan dining.

Nanma be barta tayi wani aikiba, dan ko zuba abinci hanata yayi shiya zuba sannan  yarika bata da kanshi saida ya tabbatar ta 'koshi sannan yazuba ftuit salad din a cup yatura mata gabanta shikuma yafara cin abinci.





Love u all my Fan's
[4/28, 8:42 AM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................60



*Na sadaukar da wannan page d'in gareki Asmy b Aliyu, Allah bar zumunci*




 Bayan wata d'aya cikin Hassana ya'kara girma idan ka ganta dole ka tausaya mata dan ko tafiya da kyar take iya d'aga 'kafa, hakan yasa Maman jabeer ta yanke shawarar zatayima wata tsohuwa salame a unguwarsu data Zauna gurinta tari'ka taimakamata da wasu abubuwa, Sam Hassana kin yarda tayi da zaman salame a gidanta dan lokacin da salame tafara zuwa gidan kallo d'aya Hassana tayimata taji gabanta yayi mummunan fad'uwa haka kawai taji bata bu'katar zama da ita.

Saboda haka jabeer tasamu yana Zaune d'akinsa da laptop gabansa yana kammala wani aiki na office dinsu Wanda besamu damar kammalawa jiyaba saboda dawowa yayi da wuri yayi girki yayima 'yar'lelensa wanka da gyare-gyaren gida.

Zama tayi bakin gado tare da dafe 'kungunta tana fad'in waih Allah, saurin ture laptop dindake gabansa yayi ya rungumota jikinsa yana fad'in "meya faru baniso inji kina fad'in wash wash d'innan wlh har cikin raina sai inga kamar akwai abinda ke damunki.


Murmushi tayi "ba abinda ke damuna sai nauyin cikinnan dan ba 'karamin nauyi yakeminba, tafiyama da kyar nake iya d'aga kafa, "Eyyah sorry my wife, wlh jinake kamar cikinnan yadawo jikina in'karasa miki rainonsa da haihuwarsa.

Dariya ta kyal-kyale da ita tana fad'in "wai Allah naganka da ciki, wlh bazaka kalluba, hmm barantana kuma ranar haihuwa za'asha raki danna tabbata bazaka iya jurewaba.

'Kara rungomota yayi gabansa, tare da d'ora hannunsa kan 'katon cikinta yace "inji waye yafad'amaki, aini idan da ace maza na kar6ama mata haihuwa toda kuwa bazan bari ki haifi ko d'aya da kankiba zan nunamaki ni gwarzon namiji ne, dan yayannnan goma sha biyar dukni zan haifesu.

Zaro ido tayi tare da dafe 'kirji 'ya'ya goma sha biyar a ina..........
A cikinki mana yafad'a yana 'kara had'eta da Jikinsa.
Amma baka tausayamin kallifa wahalar danakesha amma har kake fatan in'kara irinta sau sha biyar.

Murmushi yayi "ai a ina tausayinki yasa nace sha biyar amma da a yanda nakesone sonike ki haifamin dozin biyu.
Suduka dariya sukasa Hassana na fad'in ashirin da hudu kamar dai haihuwar zomaye.

Shiru yad'an ratsa na wasu 'yan mintittika, Sannan Hassana tace "my hubby akwaifa maganar dake tafe dani gurinka.
"To ina jinki, yafad'a tare da tattaro duk illahirin nutsuwarsa ya maida gareta.

"Umm dama game da maganar salame, sai kuma tayi shiru "ina jinki yafad'a "mezai hana abarta kawai ni hankalina be kwanta da zamantaba, mezai hana Nusaiba tadawo nan ko itama ai zata ri'ka taimakamin da wasu abubuwan.

"To shikenan tunda haka kikeso haka za'ayi, Ammafa kinsan ankusa bikinta saura 3 month idan lokacin yayi tatafi tabarkifa wah kuma kike tunanin za'a samo, "Ah bani fatan inkai wata ukku nan gaba ban haihuba, kaga hakan ya nunamin baka lissafi.

"Ah inji waye nikam nike lissafi nida za'a haifama babies guda hud'u lokaci guda yazan manta da lissafi.
"To shikenan yanzu dai kaba mama hakuri kada taga kamar na raina za6inta, "Kada kidamu indan mama bazataji komeba.


: Bayan wata biyu da zuwan nusaiba gidan da misalin 'karfe hud'u na yamma suna zaune suna kallon shirin *Yan Zamani* a star time tashar dad'in Kowa dan nusaiba na masifar son shirin dan ko lokacin tana gida bata ta6a bari ya wuceta, tunda suka fara kallon shirin Nusaiba ke ba Hassana labarin na baya wanda bata ganiba, amma saita lura kamar Hassanar ba saurarenta takeyiba, dan wani lokacin har d'an cije baki takeyi alamar dai akwai abinda ke damunta, lura da nusaiba tayi da Haka yasa tace "nikam Aunty sai inga kamar yau bakijin dad'in jikinnaki kodai inkira Yaya?

Kallonta Hassana tayi tare da 'ka'karo murmushin 'karfin hali tace "a'a kada ki kirashi ba wani abu inshaAllah, "ah'ah aunty kedai kadafa aje asamu matsala Yaya yaga laifina, "Hmm ba kome Nusaiba kada ki kirashi, "to shikenen tafad'a tare da ajiye wayar kusa da ita, dan da harta d'auko zatayi dialing number jabeer Hassana tahanata

Batafi minti goma da ajiye wayarba wayar tafara ringing Alamar shigowar kira, kallon Hassana tayi batare data d'au wayarba itama Hassana ita take kallo tace "yanzu danace kada ki kira saida kika kira.......

Murmushi nusaiba tayi cike dajin kunya tace "Lah wlh aunty bankirashiba, Hassana ta harareta tace "dabaki kiraba da yaza'ayi yakiraki.

"Hmm aunty kenan aibashibane yakira kallifa kigani tafad'a tana d'ago mata wayar, ganin an rubuta True love yasa Hassana tayi dariya "Hmm Abdul dinne yakira, wannan soyayya taku kamar zaku had'iye juna Allah dai yakaimu lokacin bikin.

"Hmm aunty ai duk soyayyarmu bamu kaiku keda yayaba, "yanzu dai ki d'auki wayar kada takuma tsinkewa.
Tana d'auka yake sheda mata gashinan ya iso gidan yayan nata, nan ta sanar Da Hassana Zuwanshi "Hassna tace saiki shigo dashi ko, nibari nakoma bedroom in huta.

"A'a aunty yi zamanki zamu zauna a lambu bari dai nafita da ruwa me sanyi da lemu. Wlh aunty dan kina haka amma danace yashigo Ku gaisa tafad'a tana dariyar tsokana, Hassana tace "a hakanma sai dai idan ba'ayi niyyar gaisheniba, hmm Nusiba kenan kema duka yaushe zamu ganki hakan kada ki manta yau saura wata d'aya dai-dai.

"Kai aunty kuma dan saura wata d'aya aiba daga zuwa zanzama hakaba, "Hmm Allah dai ya nunamana lokacin Hassana tafad'a "Ameen nusaiba tace tana dariya tayi saurin barin d'akin dan kada Hassanar tace tayi rashin kunya.




Love u all my Fan's ☕
[5/1, 4:01 PM] Zee Elkaseem: ๐Ÿ‘ญ *AUREN TAGWAYE* ๐Ÿ‘ญ
             ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                    ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                       ๐Ÿ•ธ๐Ÿ•ธ
                           ๐Ÿ•ธ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป



Page......................Last page ๐Ÿ‘Œ๐Ÿป





Tunda Nusaiba tafita kamar an'karomata wani matsanancin ciwon mara da ciwon baya,  tun tana daurewa harta fara nukurkusa, zuwa can taji azabar tayi yawa ta 'ko'karta ta tashi tana ta'kawa da kyar tanufi bedroom.

Tana shiga ta d'auko wayarta ta lalubo sunan jabeer ta danna kira, ringing d'aya ya d'auka dama kullum idan ze fita sai yayimata gargad'i akan dataji ciwo ko yaya takirashi.

Cikin za'kuwa dason jin mezata fad'a yace "Heelow my wife yadai? 
Cikin tsananin azabar ciwo tace "wayyo  Hubby na zan mutu ka taimakamin.........

Tana fad'in haka wani irin matsanancin ciwo yatasomata lokaci guda, saboda tsananin ciwo jikinta har kyarma yake, wani irin 'karfi yazomata lokaci guda tayi wani nishi mai 'karfi saigashi ta santalo santalelen d'anta,   kamar kuwa yana jira ya kyanyara kuka,   duk abinnan dake faruwa a kunnen Jabir Dan lokacin data kirashi tsananin ciwo yasa bata kasheba tasaki wayar.  

Shikuma can 6angaren yanata magana kawai said jin kukan jariri yayi, a firgice yatashi yanufi motarshi da sauri,

Tuki yake amma gani yake kamar ba tafiya yakeba, dan gani yayi kamar an'karama gidan nisa, 

kasa daurewa yayi, wayarshi yajawo yakuma kiranta tana d'auka takara akunne kamar azabar dataji dafarko ta'karaji nanma wani nishi tayi saiga santaleliyar yarinya, tana fad'owa ta kyanyara kuka, shima namijin datafara haihuwa kukan yake.

Jabir yaji and'au waya yanata hellow hellow yaji shiru sai kukan jarirai yakeji, ai take ya'karama motarsa gudu.



Nusaiba kuwa lokacin sukayi sallama da Abdul d'inta yatafi danta shedamashi tabaro auntynta kamar batajin dad'i.

Aiko tana shiga tundaga falo tafara jiyo kukan jarirai ai dagudu tanufi d'akin dataji kukan tana zuwa tafad'a d'akin batare da tunanin komeba.

Toxali tayi da santala-santalan baby's sunata tsala kuka, Hassana kuma tana dur'kushe kusa dasu lokacin ko cibi ba'a yankemasuba.

Nusaiba cikin tsananin mamaki tace "aunty haihuwa, kuma twowins mashaAllah,

Murmushi Hassana tayi tagayamata inda zata d'auko mata zare da reza tayi karanbani ta yanke cibi tasa zare ta daure, sannan tasakasu cikin zani tashiga kewaye tahad'a ruwan zafi wanka kawai tayi tafito.
Lokacin nusaiba tagama gyara gurin tsaf tasa morning wash tayi morping tafesa freshener lokaci d'aya d'akin yad'au kamshi.

Lokacin da jabeer ya'karaso sai taradda Hassana yayi fess da ita ba 'katon ciki, wani farinciki ya mamayeshi lokacin dayaga baby's d'inshi sunata wutsil-witsil cikin zanensu.

Godiya yayima Allah sannan yabugama mamanshi, bajimawa sai gata tazo ita ta wanke baby's lokacin labarin haihuwar Hassana yagama zaga Dangi, 

Daga can gidan su Hassana akasamo wacce ke kula dasu kullum zatayima baby's wanka tayima Hassana, har kwana bakwai.

Ranar suna ansha shagali, yara sun amsa sunansu Hassan da Hussaina.

Hussaina kuwa saida tayi kuka dan tunowa da 'yar'uwarta da yanzu itace zata haifama jabeer wannan baby's d'in.




 **             **                **





Bayan wata d'aya da haihuwar Hassana akayi bikin nusaiba, inda aka kaita unguwar g r a gidanta yahadu Bakin iya had'uwa,  Hassana ansha hidimar biki dan sune 'kirjin biki kome za'a itace gaba.

Nusiba kuwa sai nan-nan take da 'yan'biyu hotuna kau sunshasu, dan yaranne dole su burgeka yara yan wata d'aya amma idan ka gansu zakace sunyi wata ukku jikinnan nasu 6ul-bul mashaAllah.


_________________________

*Alhmdlh anan nakawo 'karshen wannan littafi nawa, gaisuwar bar girma gareku masoyana aduk inda kuke Zee Elkaseem (Mmm khady) tana tare daku sai munhad'u a sabon littafina bayan Sallah idan me kome me Kowa ya kaimu*



```Love u all my Fan's ``` ❤❤❤


SHARE THIS

Author:

Sunana Hassan Aka Amanagurus Dan Asalin Jihar Adamawa Mazaunin Garin Mubi

0 coment rios: